NSCDC TA LA’ANTA KISAN WULAKANCI NA YARINYAR SHEKARA UKU A KIYAWA, TA DAU ALAKKA NA KAMO DA HUKUNTA MASU LAIFIN

Hukumar Tsaro da Kare Muhalli ta Kasa (NSCDC), Jihar Jigawa, ta bayyana bakin cikinta tare da la’antar kisan wulakanci da aka yi wa wata yarinya ‘yar shekara uku mai suna Harira Yakubu Bala, mazauniyar unguwar Sabon Gari, karamar hukumar Kiyawa. An gano gawarta a cikin daji da safiyar Laraba, 15 ga Oktoba, 2025.

Rahotannin farko sun nuna cewa iyayenta sun bayyana rashin ganinta da misalin karfe 11:00 na safiyar Talata, 14 ga Oktoba, 2025. Abin takaici, cikin sa’o’i 24 kacal, an gano gawarta cike da raunuka da alamun cin zarafi da kisa cikin zalunci.

Bayan samun kiran gaggawa, jami’an NSCDC daga ofishin Kiyawa karkashin jagorancin Superintendent of Corps (SC) Shamsuddeen Amin suka garzaya wajen, suka kebe yankin tare da kwashe gawar don bincike da gwajin likita.

Binciken likitanci ya tabbatar da cewa an yi wa yarinyar fyade kafin a kashe ta cikin zalunci, wanda har yanzu ba a kama wadanda suka aikata wannan ta’asa ba. Hukumar ta bayyana lamarin a matsayin mugunta, rashin imani da cin zarafin dan Adam wanda ya sabawa duk wani ka’idar ɗabi’a da addini.

Shugaban Hukumar NSCDC na Jihar Jigawa, Commandant Muhammad Kabiru Ingawa, ya bayar da umarni ga sashen leken asiri da bincike na hukumar da su hada kai da ofishin Kiyawa da sauran hukumomin tsaro don tabbatar da cewa an kama wadanda suka aikata laifin, kuma an gurfanar da su a gaban kuliya.

A halin yanzu, an mika gawar marigayiyar ga iyalanta domin yi mata jana’iza bisa ka’idojin addinin Musulunci.

Commandant Ingawa ya mika sakon ta’aziyya ga

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    After PSM Report, Defence Minister Musa Justifies ₦100,000 Soldiers’ Salary, Promises Further Review

    Pix: Gen.Musa By Tunji Braimoh, Abuja Minister of Defence, General Christopher Musa (retd.), has revealed that the increase in the monthly salary of Nigerian soldiers from ₦49,000 to ₦100,000 was…

    Midnight Horror in Kaduna: Gunmen Kill Over 30 Villagers, Burn Homes in Deadly Attack

    By Usman Kabiru, Kaduna No fewer than 30 people, including women and children, have been killed following a brutal attack by suspected armed bandits on Naridon village in Kauru Local…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    After PSM Report, Defence Minister Musa Justifies ₦100,000 Soldiers’ Salary, Promises Further Review

    After PSM Report, Defence Minister Musa Justifies ₦100,000 Soldiers’ Salary, Promises Further Review

    Midnight Horror in Kaduna: Gunmen Kill Over 30 Villagers, Burn Homes in Deadly Attack

    Midnight Horror in Kaduna: Gunmen Kill Over 30 Villagers, Burn Homes in Deadly Attack

    AA Accuses INEC of Ignoring Court Judgments, Expresses Concern Over Economic Woes

    AA Accuses INEC of Ignoring Court Judgments, Expresses Concern Over Economic Woes

    Former Khana Security Chief Shot Dead by Gunmen in Rivers

    Former Khana Security Chief Shot Dead by Gunmen in Rivers

    How Blocking the Kidnappers Saved My Life During My Wife’s Abduction — Oyo School Principal’s Husband

    How Blocking the Kidnappers Saved My Life During My Wife’s Abduction — Oyo School Principal’s Husband

    The New Frontier of Economic Security: Why Nigeria’s Mining Marshals Deserve National Support

    The New Frontier of Economic Security: Why Nigeria’s Mining Marshals Deserve National Support