Atiku Ya Soki Tinubu Kan Halartar Jana’izar Siyasa Duk da Rashin Tsaro a Jihar Filato

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya soki Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa halartar abin da ya kira jana’izar siyasa a Jihar Filato maimakon ziyarar jama’ar da rikice-rikice da hare-hare suka shafa a yankin.

Atiku ya bayyana takaicinsa kan halartar Shugaba Tinubu wajen jana’izar Mama Lydia Yilwatda Goshwe, mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda. An gudanar da jana’izar ne a Jos ranar Asabar tare da halartar manyan baki da dama, ciki har da Gwamna Caleb Mutfwang da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.

Mama Lydia ta rasu a watan Agusta 2025 a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos tana da shekara 83.

Yayin da yake mayar da martani kan lamarin, Atiku ya zargi Shugaba Tinubu da rashin daidaita fifiko, inda ya ce ya kamata Shugaban Ƙasa ya yi amfani da damar ziyarar Filato wajen jajantawa iyalan da suka rasa ‘yan uwansu sakamakon hare-haren da suka addabi yankin da sauran jihohi.

“Da yawancin sassan ƙasar nan ke fama da hare-hare da asarar rayuka, abin takaici ne cewa har yanzu Shugaba Bola Tinubu bai kai ziyara ko daya ga waɗanda abin ya shafa domin nuna tausayawa ba,” in ji Atiku.

Ya bayyana cewa Jihar Filato, wadda ta fi fuskantar hare-hare a yankin Arewa ta Tsakiya, ta fi cancantar samun tausayawa da goyon baya, ba nuna siyasa ba.

“Abin bakin ciki ne cewa yayin da iyalai a Filato ke ci gaba da binne ‘yan uwansu, Shugaban Ƙasa ya zabi halartar jana’izar siyasa maimakon tsayawa tare da al’umma a lokacin da suke cikin bakin ciki,” in ji shi.

Atiku ya ƙara da caccakar abin da ya kira rashin tausayi da nuna halin ko in kula daga Tinubu da shugabancin APC, yana masu zargi da rashin mutunta darajar rayuwar ɗan Adam.

Ya kuma ambaci tashin hankali da ke ci gaba a jihohin Benue, Neja da Kwara a matsayin hujjar tabarbarewar tsaro a ƙasar, tare da suka kan gwamnatin tarayya da ta kasa kai ziyarar jaje ga mutanen da abin ya shafa.

“Ko lokacin da Shugaba Tinubu ya kai ziyara a Benue a watan Yuni, ya kauce wa garin Yelewata — cibiyar kisan kiyashi ya kuma ƙare ziyarar tasa a Makurdi,” in ji Atiku.
“Yanzu kuma, yana Jihar Filato ba don ya tausaya wa masu jinya ko ya kwantar da hankalin waɗanda suka rasa ba, sai don ya yi murnar siyasa tare da manyan jam’iyyarsa, alhali jama’a na cikin alhini. Saƙon yana da kyau: Shugaban da ke fifita jin daɗi fiye da tausayawa.”

Atiku ya ƙare da gargaɗin cewa ‘yan Najeriya na lura da irin wannan halin ko in kula daga gwamnatin Tinubu kuma ba za su manta da rashin kulawar da take nuna wa matsalar tsaro da ta addabi ƙasa ba.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    KOMANDA BRAH SAMSON UMORU YA JAJEWA JAMI’AI SU KARA NUNA KISHI DA HIMMA A AIKIN SU A LOKACIN TARON MUSTA NA LITININ

    Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula ta Ƙasa (NSCDC), Jihar Nasarawa, ta gudanar da taron ta na yau da kullum na muster a ranar Litinin, 8 ga Disamba, 2025, a…

    COMMANDANT BRAH SAMSON UMORU URGES PERSONNEL TO REDEDICATE THEMSELVES TO DUTY DURING MONDAY MUSTER PARADE

    The Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC), Nasarawa State Command, on Monday, 8th December 2025, held its routine muster parade at the Command Headquarters in Lafia, during which the…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    KOMANDA BRAH SAMSON UMORU YA JAJEWA JAMI’AI SU KARA NUNA KISHI DA HIMMA A AIKIN SU A LOKACIN TARON MUSTA NA LITININ

    KOMANDA BRAH SAMSON UMORU YA JAJEWA JAMI’AI SU KARA NUNA KISHI DA HIMMA A AIKIN SU A LOKACIN TARON MUSTA NA LITININ

    COMMANDANT BRAH SAMSON UMORU URGES PERSONNEL TO REDEDICATE THEMSELVES TO DUTY DURING MONDAY MUSTER PARADE

    COMMANDANT BRAH SAMSON UMORU URGES PERSONNEL TO REDEDICATE THEMSELVES TO DUTY DURING MONDAY MUSTER PARADE

    Ayyukan Peace Shield da Zafin Wuta: Sojojin 6 Brigade Sun Hana Fashi, Sun Ceto Mutanen da Aka Sace, Sun Kuma Kwato Makamai a Jerin Ayyuka a Fadin Taraba

    Ayyukan Peace Shield da Zafin Wuta: Sojojin 6 Brigade Sun Hana Fashi, Sun Ceto Mutanen da Aka Sace, Sun Kuma Kwato Makamai a Jerin Ayyuka a Fadin Taraba

    Operation Peace Shield/Zāfin Wuta: 6 Brigade Troops Thwart Robbery, Rescue Kidnapped Victims, and Seize Weapons in Multiple Successful Missions Across Taraba

    Operation Peace Shield/Zāfin Wuta: 6 Brigade Troops Thwart Robbery, Rescue Kidnapped Victims, and Seize Weapons in Multiple Successful Missions Across Taraba

    Olawepo-Hashim: Shugabannin Arewa Su Karɓi Alhakin Ƙarin Rashin Tsaro, Ya Yabe Tazarcen Janar Musa a Matsayin Ministan Tsaro

    Olawepo-Hashim: Shugabannin Arewa Su Karɓi Alhakin Ƙarin Rashin Tsaro, Ya Yabe Tazarcen Janar Musa a Matsayin Ministan Tsaro

    Olawepo-Hashim: Northern Leaders Must Accept Blame for Security Breakdown, Applauds Gen. Musa’s Rise to Defence Minister

    Olawepo-Hashim: Northern Leaders Must Accept Blame for Security Breakdown, Applauds Gen. Musa’s Rise to Defence Minister