Hoto: ACC Onoja
Kwamandan Rundunar Mining Marshals ta Hukumar NSCDC, ACC John Onoja Attah, ya bayyana cewa makomar masana’antar hakar ma’adanai a Najeriya na dogara ne kan ƙarfafa tsaro, aiwatar da ka’idojin lafiya da aminci, da kuma zurfafa haɗin kai da al’ummomin da ma’adanai ke cikinsu. Ya bayyana haka ne ranar Laraba yayin gabatar da jawabi a Taron Dattawan Tsaro da Lambar Girmamawa na People’s Security Monitor 2025 da aka gudanar a Nigerian National Merit Award House, Maitama, Abuja.
A cikin jawabinsa mai taken “Tsaro, Kariya, da Haɗin Kan Al’umma: Ginshiƙan Ci gaban Sashen Hakar Ma’adanai a Najeriya,” Attah ya ce sashen hakar ma’adanai yana tsaye a wani muhimmin mataki na tattalin arzikin ƙasa. Ya bayyana cewa arzikin ma’adanai da Najeriya ta mallaka ba zai iya haifar da cikakken ci gaban ƙasa ba sai an tabbatar da an samar da ingantaccen tsaro da tsarin gudanarwa mai tsafta. Ya ce, “Najeriya tana da yalwar ma’adanai, amma fitar da wannan arziki ya buƙaci tsari na tsaro, kariya, da haɗin kai da al’umma.”
Attah ya jaddada cewa tsaro shi ne ginshiƙin harkokin hakar ma’adanai a duk duniya. Ya gargadi cewa ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, satar albarkatu, da rikice-rikicen al’umma da kamfanoni na ci gaba da zama barazana ga cigaban sashen ma’adanai a Najeriya. “Wadannan barazana na kawo cikas ga samarwa, na rage kwarin gwiwar masu zuba jari, kuma na jefa ma’aikata cikin haɗari,” in ji shi. Ya ƙara da cewa Mining Marshals na NSCDC za su ci gaba da ƙoƙari wajen kare wuraren hakar ma’adanai da ma’aikata ta hanyar dabarun tsaro na zamani.
Kan batun kariya da aminci, kwamandan ya ce hakar ma’adanai aiki ne mai haɗari wanda ke buƙatar bin ka’idojin lafiya na zamani da ci gaba da horas da ma’aikata. Ya ce yawancin wuraren hakar ma’adanai na da nisan gaske da rashi ingantacciyar hanya, wanda hakan ke kara muhimmancin shiri da faɗakarwa. “Aiwatar da cikakkun matakan kariya ba zaɓi ba ne; wajibi ne don kare rayuka da tabbatar da cigaba,” in ji Attah.
Kwamandan ya kuma bayyana cewa hulɗa da al’umma muhimmin jigo ne wajen tabbatar da cigaban hakar ma’adanai na dogon lokaci. Ya ce harkar hakar ma’adanai ba za ta yi nasara ba muddin ba a damƙa wa al’umma matsayin abokan haɗin gwiwa ba. Ya bayyana cewa Mining Marshals na NSCDC sun yi aiki kafada da kafada da al’ummomi wajen magance rikice-rikice, ƙarfafa tattaunawa, da karfafa shirin tallafawa ‘yan ƙasa. “Ba za a iya samun ci gaba a harkar hakar ma’adanai idan ba tare da goyon bayan al’umma ba,” in ji shi.
Attah ya jaddada bukatar ƙarfafa dokoki da tabbatar da aiwatar da su domin samar da yanayi mai tabbas ga masu zuba jari. Ya nemi amfani da fasahar zamani irin su drones, na’urorin sa ido, da sauran kayan zamani don ƙara inganta tsaro da gano barazana tun da wuri. Ya ce ingantattun kayan aiki da kayan kariya za su rage haɗari ga ma’aikata kuma su ƙara yawan aiki.
Ya bayyana cewa horo da ƙwararrun ma’aikata na da matuƙar muhimmanci wajen kare sashen hakar ma’adanai. Ya ce ci gaba da horas da Mining Marshals, ma’aikatan sashen, da al’ummomi na taimakawa wajen magance barazanar zamani. “Ilmi, lura, da ƙwarewa su ne manyan kayan aikinmu,” in ji shi.
Attah ya kuma yi kira da ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomin tsaro, kamfanonin ma’adanai, hukumomin tsara doka da kuma al’ummomi. Ya ce ƙarin haɗin kai zai inganta musayar bayanan sirri, warware rikice-rikice, da hanzarta aiki. Haka kuma ya bukaci a samar da gaskiya da adalci a harkokin hakar ma’adanai domin rage rikice-rikice da ƙara amincewa.
Kwamandan ya kuma yi nuni da muhimmancin kare muhalli, haɗa mata da matasa, da tabbatar da ci gaban al’umma a cikin harkar hakar ma’adanai. Ya ce Mining Marshals sun fara haɗa kulawar muhalli cikin aikinsu domin tabbatar da bin ƙa’idojin kare muhalli da kare albarkatun ƙasa. Ya ce sanya mata da matasa cikin ayyukan ma’adanai na taimakawa wajen rage laifi da ƙara kwanciyar hankali a al’umma.
A ƙarshen jawabinsa, Attah ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su sabunta kudurinsu ga ginshiƙai uku da ya gabatar. Ya ce, “Nasaran sashen hakar ma’adanai na Najeriya na dogara ne kan haɗin kai. Tsaro, kariya, da haɗin kai da al’umma ba abubuwa ne daban-daban ba; ginshiƙai ne da ke gina zaman lafiya, ci gaba, da wadata.” Ya gode wa masu shirya taron bisa samar da dandalin tattauna harkokin tsaro tare da yi wa Najeriya addu’ar cigaba da zaman lafiya.



