An gudanar da wani sabon zagaye na tattaunawar zaman lafiya tsakanin hukumomin yankin da kuma ’yan bindiga da ke aiki a dazukan karamar hukumar Bakori ta Jihar Katsina a ranar Lahadi, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Karamar Hukumar, Hon. Abubakar Barde.
Taron da aka gudanar a garin Bakori an shirya shi ne domin ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai tsakanin makiyaya da al’ummomin yankin da ke fama da rikice-rikicen da suka jima suna faruwa.
Hon. Barde ya jaddada muhimmancin tattaunawa da fahimtar juna a matsayin hanyoyi mafi inganci na samun zaman lafiya mai ɗorewa, yana mai cewa ci gaba na gaske ba zai samu ba sai a cikin yanayin tsaro da kwanciyar hankali.
Ya tabbatar wa wakilan Fulani cewa gwamnatin karamar hukumar za ta ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen tabbatar da zaman lafiya, tare da roƙon su da su ba da cikakken haɗin kai ga jami’an tsaro da shugabannin al’umma domin kawo ƙarshen rikici da tashin hankali a yankin.
Sai dai wasu daga cikin mazauna yankin da kuma shugabannin gargajiya da suka halarci taron sun bayyana shakku kan tasirin irin wannan tattaunawa, suna cewa irin waɗannan ƙoƙarin a baya sun gaza kawo ƙarshen hare-haren ’yan bindiga.
Sun tuna cewa duk da yarjejeniyoyin da aka cimma a wasu sassan jihar a baya, ’yan bindiga sun ci gaba da kai hare-hare kan kauyuka, abin da ya ƙara tsoratar da jama’a da kuma rage musu amincewa da tsarin tattaunawar.
Wani daga cikin shugabannin gargajiya da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “Mun halarci tarurruka da dama na neman zaman lafiya a baya, amma ’yan bindiga ba sa cika alkawuran da suke yi. Da zarar an kammala tattaunawa, sai hare-hare su sake dawowa, mutane kuma su ci gaba da shan wahala.”
Mazauna yankin sun roƙi hukumomi da su haɗa irin waɗannan shirin zaman lafiya da ƙarin matakan tsaro na gaskiya, tare da tabbatar da cewa duk wani rukuni da ya karya yarjejeniya ya fuskanci hukunci mai tsanani.
Taron ya samu halartar shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, wakilan Fulani, da jami’an tsaro.





