…Kwamandan keshinro ya gargadi masu lalata bututun mai da masu tono rairayi ba bisa ka’ida ba a lagos
A bisa hangen nesa na babban kwamandan hukumar tsaro da kare jama’a (nscdc), farfesa ahmed abubakar audi, phd, mni, ofr, wanda ya dogara da ginshiƙai uku na aiki – haɗin kai, haɗa hannu, da daidaiton aiki – hukumar ta jihar lagos ta sake samun nasara a wani samamen da ta kaddamar.
A ranar laraba, 12 ga nuwamba, 2025, kwamandan nscdc na jihar lagos, mista adedotun keshinro, ya gabatar da sama da lita 4,000 na man fetur (pms) da aka kama daga hannun masu fataucin man da suka yi ƙoƙarin satar shi ta hanyoyi da kuma ta ruwa a yankin badagry na jihar.
Wannan samame ya biyo bayan sahihin bayani da rundunar ta badagry division ƙarƙashin jagorancin chief superintendent of corps ekunola gbenga ta samu a ranar jumma’a, 7 ga nuwamba, 2025. Rundunar ta yi gaggawar kai farmaki inda ta tarwatsa wasu ‘yan ta’annati da aka sani da satar man fetur a yankin. Da suka ga jami’an tsaro, sai suka tsere suka bar jarkoki 150 na lita 25 kowanne da wasu kwalaben ragolis cike da man fetur, da wasu jarkoki da ake shirin cikawa kafin jami’an suka iso.
Kwamandan keshinro ya kuma gode wa rundunar sojan ruwa ta najeriya saboda mika jarkoki 73 na lita 25 na man pms da suka kwato ga sashen badagry na nscdc, yana jaddada irin kyakkyawar alaƙa da haɗin kai da ke tsakanin hukumomin tsaro a jihar lagos.
Yayin da yake magana da ‘yan jarida, kwamandan keshinro ya gargadi masu lalata bututun mai da masu satar albarkatun ƙasa da su daina waɗannan ayyukan ta’annati, musamman a wannan ƙarshen shekara da ake yawan samun irin waɗannan laifuka. Ya bayyana cewa hukumar za ta mayar da martani mai ƙarfi ga duk wanda aka kama da irin wannan laifi.
Kwamandan ya kuma ja kunnen masu tono rairayi ba bisa ka’ida ba ƙarƙashin gadajen third mainland, carter, da eko, da su gaggauta daina, domin irin wannan aiki yana iya lalata tsari da ƙarfafa gadar, tare da jawo haɗarin rayuka da lalata muhimman kayan gwamnati.
Ya kuma tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da aiki tukuru wajen kare muhimman kadarorin ƙasa da gine-ginen gwamnati (critical national assets and infrastructure) a jihar lagos. A wani ɓangare na wayar da kai da haɗin gwiwa da al’umma, hukumar za ta kaddamar da shirin masu ruwa da tsaki a yammacin lagos a ranar talata, 18 ga nuwamba, 2025, domin ƙarfafa haɗin gwiwa da wayar da kan jama’a.
Hukumar nscdc ta jihar lagos ta tabbatar wa jama’ar jihar da cikakken kudirinta na ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki don hana duk wani nau’in barna da zai iya kawo cikas ga zaman lafiya, tsaro, da walwalar jama’a.



