KWARA TA KARYATA IKIRARIN MAMAYE JIHAR DA ’YAN BINDIGA, TA ZARGI PETER OBI DA YAƊA LABARAN KARYA KAN TSARO

Gwamnatin Jihar Kwara ta karyata rahotannin da ke cewa ’yan bindiga sun mamaye kananan hukumomi tara a jihar, tana bayyana wannan ikirari a matsayin ƙarya da kuma yaudara ga jama’a.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Hajiya Bolanle Olukoju, ta fitar a ranar Talata, gwamnati ta kuma zargi wasu ’yan adawa, ciki har da Mista Peter Obi, da amfani da dandamalin su wajen yaɗa labaran ƙarya game da halin tsaro a jihar Kwara.

Sanarwar ta ce: “Muna so mu sanar da jama’a cewa wani labari mara tushe na cewa kananan hukumomi tara a Jihar Kwara suna ƙarƙashin mamayar ’yan bindiga yana yawo a kafafen sada zumunta. Wannan ƙarya ce! Babu wani ɓangare na jihar da ke ƙarƙashin ikon ’yan bindiga.”

Hajiya Olukoju ta bayyana cewa duk da cewa akwai wasu matsalolin tsaro a wasu yankuna kaɗan, ba su kai matsayin da za a ce an mamaye jihar ba kamar yadda ake yada ƙaryar.

Ta ƙara da cewa: “Muna da hujjoji masu karfi da ke nuna cewa waɗanda ke yada irin waɗannan labaran ƙarya na goyon bayan miyagu ne, suna nufin su tada hankalin jama’a da kuma raunana kwarin gwiwar al’umma.”

Sanarwar ta kuma nuna takaici ga Mista Peter Obi, inda ta zarge shi da yada wannan labari mara tushe a shafukan sada zumuntar sa.

“Abin takaici ne ganin cewa Mista Peter Obi ya yi amfani da shafukan sa na sada zumunta wajen yada wannan labarin ƙarya. Wannan dabi’a ba ta dace da mutum mai matsayin ɗan kasa nagari ba. Muna roƙonsa da ya goge wannan rubutu domin ba gaskiya ba ne kuma yana iya haifar da tashin hankali,” in ji sanarwar.

Kwamishinar ta roƙi jama’a da su rika tantance gaskiyar bayanai kafin su yada su, tana gargaɗi cewa irin waɗannan labaran ƙarya na iya ƙara damuwa da wahalar da jami’an tsaro wajen gudanar da aikinsu.

“Irin wannan rashin hankali yana ƙara wahalar da jami’an tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya. Don haka muna kira ga ’yan kasa da su goyi bayan gwamnati ta hanyar ƙin yarda da kuma bayar da rahoton duk wani labarin ƙarya,” sanarwar ta ƙare.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    Mining Marshals Petition Reps Speaker, Dismiss Corruption Allegations as Politically Motivated Smear CampaignWriting

    Pix: ACC John Attah Onoja, Head, NSCDC Mining Marshals By Isiaka Mustapha, Editor-in-Chief, People’s Security Monitor The Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC) Mining Marshals have petitioned the Speaker…

    Blood, Power and Billions: Why Violence Continues to Haunt Nigeria’s Transport Union System

    By Isiaka Mustapha, Editor-in-Chief, People’s Security Monitor The recurring killings of prominent figures within the National Union of Road Transport Workers (NURTW) have exposed a troubling pattern of violence that…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Mining Marshals Petition Reps Speaker, Dismiss Corruption Allegations as Politically Motivated Smear CampaignWriting

    Mining Marshals Petition Reps Speaker, Dismiss Corruption Allegations as Politically Motivated Smear CampaignWriting

    Blood, Power and Billions: Why Violence Continues to Haunt Nigeria’s Transport Union System

    Blood, Power and Billions: Why Violence Continues to Haunt Nigeria’s Transport Union System

    Federal Fire Service Trains 5,300 Army Recruits on Fire Prevention and Emergency Response in Osun

    Federal Fire Service Trains 5,300 Army Recruits on Fire Prevention and Emergency Response in Osun

    NUJ FCT Pledges Support for Police Complaint Response Unit, Strengthens Accountability Monitoring

    NUJ FCT Pledges Support for Police Complaint Response Unit, Strengthens Accountability Monitoring

    MC Oluomo Challenges Adeleke’s Suspension of NURTW in Osun, Says Governor Lacks Legal Authority

    MC Oluomo Challenges Adeleke’s Suspension of NURTW in Osun, Says Governor Lacks Legal Authority

    NIS Comptroller-General Charges Public Relations Officers to Enhance Service Delivery Through Professional Training

    NIS Comptroller-General Charges Public Relations Officers to Enhance Service Delivery Through Professional Training