Rundunar Sojojin Najeriya ta bayyana gagarumar nasara a yakin da take yi da ta’addanci da ‘yan fashi a sassan ƙasar, inda ta kashe dama-daman ‘yan ta’adda, ta kama mutane 450 da ake zargi, tare da ceto mutane 180 da aka yi garkuwa da su cikin watan Satumba kaɗai.
Daraktan Hulɗa da Jama’a na Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar a Abuja, inda ya bayyana irin nasarorin da dakarun soji suka samu a fadin ƙasar cikin watan.
A cewar Kangye, jimillar ‘yan ta’adda 39 sun miƙa wuya ga dakarun soji, yayin da aka kwato makamai iri 63 da harsasai 4,475 a lokuta daban-daban na aikin tsabtace yankuna. Ya ƙara da cewa, an kuma kwato grenades, abubuwan hada bama-bamai (IEDs), na’urorin sadarwa, motocin hawa, babura, da kayan aiki da ‘yan ta’adda ke amfani da su wajen aikata laifuka.
Kangye ya ce, dakarun haɗin gwiwa na Operation HADIN KAI da ke Arewa maso Gabas sun ci gaba da kai hare-hare kan mayakan Boko Haram da ISWAP a jihohin Borno, Yobe, da Adamawa. Sojojin sun kashe da dama daga cikin ‘yan ta’adda, sun kama mutane 21 da ake zargi da taimaka musu, tare da kwato makamai da harsasai masu yawa a yankunan Konduga, Gwoza, Mafa, Monguno, Damboa, Biu da Kukawa. Wannan aikin ya haifar da rushe sansanonin ‘yan ta’adda da katse hanyoyin samar musu da kayan aiki, tare da taimaka wa ‘yan gudun hijira su koma gidajensu.
A Arewa maso Yamma, dakarun Operation FANSAN YAMMA sun gudanar da nasarorin farmaki a jihohin Zamfara, Sokoto, Kebbi, Katsina da Kaduna, inda suka kashe da dama daga cikin ‘yan bindiga, suka kama mutane 46, ciki har da shugaban wata ƙungiyar ta’addanci, Ali Saidu. Haka kuma, an ceto mutane 13 da aka sace, tare da katse hanyoyin samar da kayayyakin aiki ga ‘yan fashi a Maradun, Isa, da Sabon Birni.
A ƙarƙashin Operation ENDURING PEACE, sojoji sun amsa kiran gaggawa a jihohin Filato da Kaduna, inda suka kashe masu ta’addanci da dama, suka kama mutane 12, tare da ceto mutane hudu da aka yi garkuwa da su. Haka kuma, dakarun Operation WHIRL STROKE sun kashe ‘yan bindiga, suka kama mutane shida a jihohin Benue, Taraba, Kogi, da Nasarawa, har ma da wasu yankuna na Babban Birnin Tarayya, inda suka ceto mutane biyu da aka yi garkuwa da su.
A Kudu maso Gabas, dakarun Operation UDO KA sun kashe ‘yan tawaye, suka kama mutane hudu a jihohin Anambra da Imo, inda suka kwato makamai, harsasai, motocin hawa, da bama-bamai.
Manjo Janar Kangye ya jaddada cewa sojojin ƙasa za su ci gaba da jajircewa wajen dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a ƙasar, ta hanyar haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da sojojin haɗaka. Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da kai hare-haren da aka tsara bisa bayanan sirri har sai an samu cikakken zaman lafiya a sassan Najeriya.





