Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya (CGF), Olumode Samuel Adeyemi, a ranar Litinin 16 ga Fabrairu, 2026, ya ziyarci wurin da gobara ta tashi a Kasuwar Singa da ke Kano domin tantance abin da ya faru tare da fara daukar matakan kariya, bisa umarnin Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo.
Ziyarar ta kasance wani bangare na shirin karfafa tsarin tsaro daga gobara a manyan cibiyoyin kasuwanci a jihar, biyo bayan gobarar da ta faru a ranar Asabar. A halin yanzu, jami’an kashe gobara na ci gaba da aikin yayyafa ruwa domin tabbatar da cewa gobarar ba ta sake kunno kai ba.
Yayin duba wurin, Shugaban Hukumar ya tantance yadda aka gudanar da aikin ceto tare da ganawa da jami’an da ke bakin aiki. Ya yaba da jajircewarsu da kwarewarsu wajen shawo kan gobarar da kuma kare dukiyoyin da ke makwabtaka da wurin.
A ci gaba da tuntubar masu ruwa da tsaki, Adeyemi ya gana da shugabannin Kungiyar Ci gaban Kasuwar Singa (SIMDA) da kuma Kungiyar ’Yan Kasuwar Abubakar Rimi (AMATA), wadanda suka tarbe shi tare da tawagarsa. Tattaunawar ta mayar da hankali kan hanyoyin da za a bi domin rage hadarin gobara a kasuwannin da ke cike da jama’a.
Da yake jawabi, CGF ya isar da damuwar Ministan Harkokin Cikin Gida kan lamarin, tare da bayyana shirin kafa tashoshin kashe gobara a muhimman kasuwanni a fadin Jihar Kano. Ya ce wannan mataki zai rage lokacin kai dauki tare da samar da dindindin kasancewar jami’an kashe gobara a cibiyoyin kasuwanci.
Ya kuma jaddada muhimmancin hadin kai tsakanin ’yan kasuwa da Hukumar Kashe Gobara, yana mai cewa kariya daga gobara na bukatar daukar alhaki tare, kai rahoton gaggawa cikin lokaci da kuma bin dokokin tsaro yadda ya kamata.
Shugabannin SIMDA da AMATA sun yi maraba da wannan shiri tare da yin alkawarin ba da cikakken hadin kai ga Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya domin samar da kasuwanni masu aminci da kariya.




