Jakadan Tarayyar Afrika mai kula da Harkokin Siyasa, Zaman Lafiya da Tsaro (AU CPAPS), Mai Girma Ambasada Bankole Adeoye, ya kai ziyarar girmamawa ga Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwa, Vice Admiral Idi Abbas, a Hedikwatar Rundunar Sojin Ruwa da ke Abuja, a ranar 5 ga Fabrairu, 2026.
A yayin ziyarar, Ambasada Adeoye ya taya Vice Admiral Idi Abbas murna kan gagarumin nasarorin da Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya ta samu a fannin tsaron teku. Ya yabawa Rundunar bisa nasarar dakile hare-haren fashin teku a ruwan Nijeriya tun daga shekarar 2022, lokacin da aka cire Nijeriya daga jerin kasashen da ke fama da fashin teku na Hukumar International Maritime Bureau (IMB). Haka kuma, Jakadan ya yabawa rawar da Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya ke takawa wajen yaki da laifukan ketare iyaka ta hanyar hadin gwiwa da sauran rundunonin sojin ruwa a yankin Tekun Guinea.
Ambasada Adeoye ya jaddada cewa wadannan kokari na Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya na da matukar muhimmanci yayin da Afirka ke rungumar Yarjejeniyar Ciniki ta Nahiyar Afirka (AfCFTA), wadda ke da burin hade tattalin arzikin kasashe 55 da kafa babbar kasuwar ciniki mafi girma a duniya. Ya bayyana cewa tabbatar da tsaron teku na da muhimmanci wajen kare harkokin kasuwanci, zuba jari da bunkasar tattalin arziki a fadin nahiyar.
A yayin taron, Jakadan AU CPAPS ya gabatar da shawarar shirya atisayen sojin ruwa na Afirka baki daya a shekarar 2027 domin karfafa hadin gwiwa tsakanin rundunonin sojin ruwa na kasashen Afirka. Ya bukaci Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya da ta ci gaba da jagoranci, musamman ganin rahoton Global Firepower na baya-bayan nan da ya bayyana Nijeriya a matsayin kasa mai karfin rundunar sojin ruwa mafi girma a Afirka. Ya nemi goyon bayan Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya wajen shirin Tarayyar Afrika na karbar bakuncin atisayen sojin ruwan na nahiyar baki daya, wanda zai hada da rundunonin sojin ruwa daga kasashen abokan hulda a duniya. Bugu da kari, Jakadan ya roki Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya da ta yi la’akari da shirya atisayen sojin ruwa na yankin da zai hada rundunonin sojin ruwa na ECOWAS Maritime Zone E da sauran masu sha’awa, domin inganta tsaron teku, zama abin koyi ga atisayen gaba, da kuma fadada hadin gwiwa a fadin nahiyar.
A nasa bangaren, Vice Admiral Idi Abbas ya tarbi Ambasada Adeoye hannu bibbiyu tare da yabawa Tarayyar Afrika kan jajircewarta wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Afirka. Ya bayyana cewa Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya za ta duba shawarar shirya atisayen sojin ruwa na yankin tare da kasashen mambobin ECOWAS Maritime Zone E a karkashin tsarin Combined Maritime Task Force. Babban Hafsan Rundunar Sojin Ruwan ya sake jaddada kudurin Rundunar na ci gaba da daukar matakan tabbatar da tsaron tekun Nijeriya daga dukkan nau’ikan laifuka da ayyukan haramtattu.




