Ɗan takarar shugaban ƙasa kuma fitaccen ɗan kasuwa a duniya, Dr. Gbenga Olawepo-Hashim, ya yi kira ga manyan shugabannin Arewa da su karɓi alhakin tabarbarewar tsaro da ke ci gaba da addabar yankin.
Ya kuma yi maraba da naɗin Janar Christopher Musa a matsayin sabon Ministan Tsaro, yana kira da a mayar da wannan dama ta gwamnati zuwa ga sakamako na zahiri.
A wata sanarwa da ya fitar jiya, Olawepo-Hashim ya ce ya kalli tantancewar da aka yi wa Janar Musa a Majalisar Dattawa, inda ya burge shi da gaskiya, hangen nesa da kuma jajircewarsa ga aikin kasa.
“Ina kallon tantancewarsa a Majalisar Dattawa. Na ga bayyanannen jajirci da kishin kasa a tare da shi. Ina fatan gwamnati za ta ba shi goyon baya matuƙa domin ya yi nasara,” in ji shi.
Sai dai ya gargadi cewa ’yan Najeriya—da ma masana tsaro a duniya—sun gaji da jin alkawura marasa tabbaci daga manyan ’yan siyasa. Ya ce jama’a na son a ga gaggawar matakai, ba tsagwaron magana ba, domin kawo ƙarshen kashe-kashe, sace-sace da kuma faɗaɗa yankin da ’yan ta’adda ke kokarin mamaye a Arewa.
“Wannan ba lokaci ba ne na alamar siyasa; lokaci ne na aiki. ’Yan Najeriya na son mataki kai tsaye, ba yaudarar jama’a ta ziyara ko hayaniya a kafafen yada labarai ba. Wannan naɗi dole ne ya zama hanyar samar da manufofi, tsare-tsare da sakamako a aikace,” in ji shi.
Ya yi kira ga fadar shugaban ƙasa da Majalisar Dokoki su hanzarta amincewa da dokar kafa ’yan sandan jihohi da kananan hukumomi, yana mai jaddada cewa ba za a samu dorewar tsaro ba sai an gina karfi da tsarin tsaro na cikin al’umma.
Haka kuma ya ce dole ne shugabannin Arewa su fuskanci gaskiyar cewa shekaru na gazawar mulki ne suka tilasta dubban matasa shiga hannun ƙungiyoyin da ke ɗaukar makamai.
“Yawaitar shiga ƙungiyoyin ta’addanci ba abin mamaki ba ne. Rashin aikin yi da talauci—da mulki mara inganci a matakin jihohi da kananan hukumomi—sun ba da gagarumin gudummawa. Duk da cewa rikicin yankin Sahel ya yi tasiri, mun ƙara wa kanmu matsala da mulki mara tsari,” in ji shi.
Yayin da yake tunawa da zamanin Firayim Minista Sir Ahmadu Bello, Aminu Kano, Joseph Tarka da Sir Kashim Ibrahim, ya ce wancan zamanin ya fi na yanzu tsaro, daidaito da nagartar shugabanci.
“A lokacin su, Arewa ta fi aminci, ta fi zaman lafiya, ta kuma fi samun shugabanni masu gaskiya da rikon amana. Yanzu kuwa, da yawa daga shugabanni sun koma rayuwa irin ta attajiran man fetur, yayin da talakawa ke cikin ƙuncin rayuwa,” ya kara da cewa.
Olawepo-Hashim ya kammala da kira ga sabon tsarin shugabanci a Arewa.
“Lokaci ya yi da Arewa za ta kawar da shugabannin da suke ƙara wa kansu arziki, amma suka bar jama’arsu a talauce, suna riƙe da mulki ta hanyar amfani da kabilanci da addini,” in ji shi.



