NSCDC Ta Kama Mutane 20 Bisa Laifin Ta’addanci, Garkuwa da Mutane, Lalata Kayan Gwamnati da Zamba, Ta Gano Makamai da Alburusai


Rukuni na Musamman na Leken Asiri na Babban Kwamandan Hukumar Tsaro ta Fararen Hula (NSCDC) ya kama mutane 20 da ake zargi da aikata laifukan ta’addanci, garkuwa da mutane, lalata muhimman kayan gwamnati, zamba da sauran laifuka a Abuja (FCT), Nasarawa, Benue, Plateau da Jihar Ondo.

A cewar sanarwar, an gudanar da wannan samamen ne bisa umarnin Babban Kwamandan NSCDC, Farfesa Ahmed Abubakar Audi, tsakanin watan Oktoba da Nuwamba, 2025, inda aka samu nasarar cafke gungun ’yan ta’adda da masu aikata manyan laifuka.

Kayan da aka kwato sun haɗa da bindigogi AK-47 guda biyu, G3 guda biyu, harsasai sama da 105, mota Toyota Corolla, babura guda hudu, wayoyin hannu, kayan lantarki, tsafi da kuɗi.

Kwamandan rukunin, AS Dandaura, ya bayyana cewa daga cikin waɗanda aka kama, akwai mutum biyu da aka tabbatar da cewa suna da alaƙa da ƙungiyoyin ta’addanci da ke da hannu a hare-haren kabilanci a wasu yankuna na jihohin Benue da Plateau. Haka kuma, an kama wasu biyar da ake zargin manyan masu sayen kayayyakin da aka sata, da wasu da ke da hannu a lalata kayan gwamnati, fashi da makami da zamba.

Daga cikin wadanda aka kama akwai Ibrahim Hudu (mai shekaru 30) da Hassan Ibrahim (mai shekaru 23) waɗanda suka amsa laifin yin garkuwa da mutane da kisa a Jihar Nasarawa. Sun bayyana yadda suka yi garkuwa da suka kashe Mista Obasanjo H. Aku da Mista Muhammadu Yaka duk bayan karɓar kudin fansa. Bincike ya kuma nuna cewa Hassan Ibrahim na da hannu a hare-haren ’yan bindiga a Guma (Benue) da Qua’an-Pan (Plateau).

A Jihar Ondo kuma, NSCDC ta kama wani Iseoluwa Shadrach Omosehin mai shekaru 27 da bindigogin G3 guda biyu. Haka nan a Nasarawa, an kama wasu da ke lalata kayan wutar lantarki da kuma karɓar kudin wuta daga mazauna unguwa ta hanyar zamba.

Kwamandan Dandaura ya ce an kuma kama wasu mutane biyar da ke sayen kayayyakin da aka sata daga ’yan fashi da masu garkuwa da mutane, domin karya tsarin kuɗaɗen su.

Ya jaddada cewa Babban Kwamandan NSCDC, Farfesa Audi, ya kuduri aniyar ci gaba da yaki da masu aikata laifuka da masu lalata arzikin ƙasa, tare da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa. Ya ce duk wanda aka kama za a gurfanar da shi gaban kotu bayan kammala bincike, sannan ya bukaci jama’a su ci gaba da bai wa jami’an tsaro bayanan sirri domin kawo ƙarshen aikata laifuka a ƙasar nan.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    NSCDC Ondo Decorates 110 Promoted Officers

    The Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC), Ondo State Command, has decorated 110 officers recently promoted in the 2025 promotion exercise.The decoration ceremony was presided over by the State…

    NSCDC Lagos Decorates 200 Promoted Officer

    The Lagos State Command of the Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC) on Thursday decorated 200 officers recently promoted in the 2025 promotion exercise.The decoration ceremony, held at the…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    NSCDC Ondo Decorates 110 Promoted Officers

    NSCDC Ondo Decorates 110 Promoted Officers

    NSCDC Lagos Decorates 200 Promoted Officer

    NSCDC Lagos Decorates 200 Promoted Officer

    CCS Reaffirms Commitment to Stronger Partnership with NAFRC

    CCS Reaffirms Commitment to Stronger Partnership with NAFRC

    Chief of Naval Staff Attends DIMDEX 2026 to Enhance Nigerian Navy’s Maritime Capabilities

    Chief of Naval Staff Attends DIMDEX 2026 to Enhance Nigerian Navy’s Maritime Capabilities

    Strengthening Security–Education Collaboration: NSCDC, TETFund Move Toward Strategic Partnership

    Strengthening Security–Education Collaboration: NSCDC, TETFund Move Toward Strategic Partnership

    Federal Fire Service Controller Attends NSCDC Promotion Decoration Ceremony in Kebbi

    Federal Fire Service Controller Attends NSCDC Promotion Decoration Ceremony in Kebbi