Sojojin Najeriya Sun Ceto Mutane 17 da Aka Sace, Sun Kama Masu Zargi 20 a Fadin Kasa

Sojojin Najeriya sun ƙara ƙaimi a ayyukansu na yaki da ‘yan ta’adda da kungiyoyin masu laifi a fadin ƙasar, inda suka ceto mutane 17 da aka sace, suka kama mutane 20 da ake zargi, tare da kashe ‘yan ta’adda biyu cikin sa’o’i 48 da suka gabata.

A wata sanarwa da rundunar sojin ta wallafa a shafinta na X a ranar Asabar, ta bayyana cewa an gudanar da wadannan hare-hare cikin tsari a yankunan Arewa maso Gabas, Arewa maso Yamma, Arewa ta Tsakiya, da Kudu maso Kudu.

Sanarwar ta bayyana cewa sojojin bataliya ta 192 a Arewa maso Gabas tare da hadin gwiwar kungiyar Civilian Joint Task Force sun fafata da mayakan ISWAP da Boko Haram a kauyen Hudugum da ke karamar hukumar Gwoza, Jihar Borno, inda aka kashe ‘yan ta’adda biyu.

Sojojin sun kuma bayyana cewa wasu ‘yan ta’adda uku – Fannami Ari (wanda ake kira Abu Dujana), Hussaini Hassan Modu (Abu Yusuf), da wani sabon dan ta’adda da ba a bayyana sunansa ba – sun mika wuya ga dakarun soji a yankunan Kukawa da Damboa, suna mai cewa sun gaji da shugabanninsu da kuma mummunan yanayin rayuwa a sansanoninsu.

A yankin Arewa maso Yamma, sojojin brigade ta 1 sun hana sace mutane a cikin Jihar Zamfara, inda suka ceto mutane 11 a lokuta daban-daban a kan hanyoyin Magami–Jan Gemi da Kucheri–Bilbis. Wadanda aka ceto sun riga sun hadu da iyalansu.

A Arewa ta Tsakiya, dakarun da ke karkashin ayyukan Enduring Peace da Whirl Stroke sun kai samame a jihohin Filato, Benue, Nasarawa, da Kaduna, inda suka kama mutane 15 da ake zargi da shiga harkar kungiyoyin asiri, garkuwa da mutane, sata da rikice-rikicen kabilanci. Haka kuma, an ceto wasu mutane 4 da aka sace a yayin aikin.

A yankin Kudu maso Kudu kuwa, sojojin sun gano kuma suka rusa wuraren tace danyen mai biyu da ake amfani da su ba bisa doka ba a Biseni, karamar hukumar Yenagoa ta Jihar Bayelsa. Haka kuma sun kama jakunkuna 62 na danyen mai da aka sace, wanda kimarsa ta kai lita 3,000 a karamar hukumar Ohaji/Egbema ta Jihar Imo.

“Sojojin Najeriya suna nan daram cikin kudurinsu na yaki da dukkan makiyan kasa da kuma kare ikon da hadin kan kasar,” in ji sanarwar.

A baya, a ranar 17 ga Oktoba, 2025, sojojin Najeriya sun ceto mutane 21 da aka sace, ciki har da ‘yan kasar China hudu, a wani samame da suka gudanar a jihohin Kwara da Kogi.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    Ayyukan Peace Shield da Zafin Wuta: Sojojin 6 Brigade Sun Hana Fashi, Sun Ceto Mutanen da Aka Sace, Sun Kuma Kwato Makamai a Jerin Ayyuka a Fadin Taraba

    Sojojin 6 Brigade na Rundunar Sojin Najeriya Sector 3 Operation Whirl Stroke sun samu muhimman nasarori a fagen aiki karkashin Ayyukan Peace Shield da Zafin Wuta, inda suka kaddamar da…

    Operation Peace Shield/Zāfin Wuta: 6 Brigade Troops Thwart Robbery, Rescue Kidnapped Victims, and Seize Weapons in Multiple Successful Missions Across Taraba

    Troops of the 6 Brigade, Nigerian Army/Sector 3 Operation Whirl Stroke, have recorded major operational breakthroughs under the ongoing Operations Peace Shield and Zāfin Wuta. A series of coordinated missions…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ayyukan Peace Shield da Zafin Wuta: Sojojin 6 Brigade Sun Hana Fashi, Sun Ceto Mutanen da Aka Sace, Sun Kuma Kwato Makamai a Jerin Ayyuka a Fadin Taraba

    Ayyukan Peace Shield da Zafin Wuta: Sojojin 6 Brigade Sun Hana Fashi, Sun Ceto Mutanen da Aka Sace, Sun Kuma Kwato Makamai a Jerin Ayyuka a Fadin Taraba

    Operation Peace Shield/Zāfin Wuta: 6 Brigade Troops Thwart Robbery, Rescue Kidnapped Victims, and Seize Weapons in Multiple Successful Missions Across Taraba

    Operation Peace Shield/Zāfin Wuta: 6 Brigade Troops Thwart Robbery, Rescue Kidnapped Victims, and Seize Weapons in Multiple Successful Missions Across Taraba

    Olawepo-Hashim: Shugabannin Arewa Su Karɓi Alhakin Ƙarin Rashin Tsaro, Ya Yabe Tazarcen Janar Musa a Matsayin Ministan Tsaro

    Olawepo-Hashim: Shugabannin Arewa Su Karɓi Alhakin Ƙarin Rashin Tsaro, Ya Yabe Tazarcen Janar Musa a Matsayin Ministan Tsaro

    Olawepo-Hashim: Northern Leaders Must Accept Blame for Security Breakdown, Applauds Gen. Musa’s Rise to Defence Minister

    Olawepo-Hashim: Northern Leaders Must Accept Blame for Security Breakdown, Applauds Gen. Musa’s Rise to Defence Minister

    “Muna Tare da Ku”: Gwamna Zulum Ya Karfafa Guiwar Sojoji a Ziyara Damboa

    “Muna Tare da Ku”: Gwamna Zulum Ya Karfafa Guiwar Sojoji a Ziyara Damboa

    “We Stand Firmly With You”: Governor Zulum Encourages Troops During Visit to Damboa

    “We Stand Firmly With You”: Governor Zulum Encourages Troops During Visit to Damboa