Majalisar Tarayya ta Najeriya ta yaba wa Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa (FFS) bisa jajircewarta wajen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa, da kuma ci gaba da aiwatar da manufofin tsaron gobara a ƙasar nan. Wannan yabo ya fito ne daga Kwamitin Majalisar Tarayya kan Ka’idojin Tsaro da Dokoki, yayin wani taron sauraron jama’a a majalisar.
A yayin taron, Kwamandan Janar na Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa, Olumode Adeyemi Samuel, ya gabatar da shirin sauye-sauyen da hukumar ke aiwatarwa tare da bayyana wuraren da take bukatar hadin kai daga bangaren majalisa da manufofin gwamnati.
A nasa jawabin, Shugaban Kwamitin, Hon. David Idris Zakaria, ya yaba da irin sadaukarwar Hukumar Kashe Gobara wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma a fadin kasar. Ya bayyana cewa kwamitinsu ya kara tabbatar da matakan tsaro a cikin ginin majalisa, ciki har da ware filin ajiye motoci a matsayin wurin taro idan gobara ko wata gaggawa ta faru.
Hon. Zakaria ya jaddada cewa manufar kwamitinsu tana da kamanceceniya da ta Hukumar Kashe Gobara — dukkansu suna aiki ne don kare ‘yan Najeriya da inganta tsaron kasa. Ya kuma jawo hankali kan bukatar ci gaba da hadin gwiwa tsakanin majalisa da hukumar don tabbatar da ingantaccen tsarin rigakafi da amsa matsalar gobara a duk fadin Najeriya.
A yayin tattaunawar, mambobin kwamitin sun nuna sha’awar su kan ayyukan Hukumar Kashe Gobara, tsare-tsaren sauye-sauyenta, da kalubalen da take fuskanta. Sun kuma nemi karin bayani kan Sabon Dokar Hukumar Kashe Gobara, wacce ke cikin tsarin duba dokoki, tare da alkawarin bayar da cikakken goyon baya domin tabbatar da hanzarin amincewarta ta zama doka.
Kwamitin ya kara tabbatar da shirinsa na yin aiki tare da Hukumar Kashe Gobara wajen samar da daftarin National Fire Safety Code, domin karfafa matakan tsaro, inganta sa ido, da kuma yada al’adar rigakafin gobara a duk fadin kasar nan.



