Hoto: Gwamna Inuwa Yahaya
Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, an zaɓe shi domin karɓar lambar yabo ta 2026 ta “Jiha Mafi Amintacciya a Najeriya” a babban taron shekara-shekara na People’s Security Monitor (PSM) da kuma bikin bayar da kyaututtuka da za a gudanar a Abuja.
Masu shirya taron sun bayyana cewa wannan karramawa ta samo asali ne daga gagarumar jajircewar gwamnan wajen tafiyar da harkokin tsaro, tabbatar da zaman lafiya, gina sulhu tsakanin al’umma, da kuma matakan hana aikata laifuka, wanda ya sanya Gombe ta kasance ɗaya daga cikin jihohin da suka fi kwanciyar hankali a ƙasar nan.
A cewar masu shirya taron, gwamnatin Gwamna Yahaya ta nuna shugabanci mai ƙarfi ta hanyar ƙarfafa ayyukan tsaro da ke dogara da bayanan sirri, tallafa wa hukumomin tsaro, inganta zaman lafiya tsakanin al’umma, da samar da yanayi mai kyau ga ci gaban tattalin arziki da zuba jari. Sun kuma yaba masa bisa yadda yake gudanar da shugabanci cikin tsari da kuma haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki wajen tabbatar da zaman lafiya a jihar.
Taron zai ja hankalin manyan jami’an gwamnati, shugabannin sojoji da hukumomin tsaro, masu tsara manufofi, sarakunan gargajiya, jami’an diflomasiyya, ‘yan jarida, da ƙwararrun masana tsaro daga sassa daban-daban na Najeriya da ma ƙetare.
A cikin manyan abubuwan da za su gudana, Gwamna Yahaya zai kasance ɗaya daga cikin manyan masu gabatar da sabon littafi mai taken “Mai Kare Ƙasa: Yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ya Shafe Shekaru Uku Yana Yaƙi da Rashin Tsaro, Shawarwari Masu Tsauri, Sadaukarwa da Nasarori.” Littafin mai babi 21, wanda Isiaka Mustapha ya wallafa, ya nazarci ƙalubalen tsaro a Najeriya, matakan yaƙi da ta’addanci na gwamnatin Tinubu, da kuma haɗin gwiwar hukumomi wajen magance rashin tsaro a faɗin ƙasa.
Haka kuma, ana sa ran gwamnan zai gabatar da muhimmin jawabi kan tafiyar da harkokin tsaro, haɗin gwiwar hukumomin tsaro, da kuma hanyoyin da suka shafi al’umma wajen tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa da kwanciyar hankali a ƙasa baki ɗaya. Masu shirya taron sun bayyana cewa gudunmawar da gwamnan ke bayarwa ta sa ya samu girmamawa da karramawa a matakin ƙasa.
Za a gudanar da Taron Tsaro na PSM na 2026 a ranar Alhamis, 4 ga Yuni, 2026, da ƙarfe 10:00 na safe a zauren Nigeria National Merit Award House, Maitama, Abuja, ƙarƙashin jagorancin bako na musamman, Manjo Janar Christopher Musa (Rtd), Ministan Tsaro na Najeriya.
Masu shirya taron sun ƙara da cewa za a gudanar da tattaunawa kan manufofin tsaro, jawaban taya murna, gabatar da littafin, da kuma bayar da kyaututtuka ga fitattun mutane da hukumomi da ke bayar da gudunmawa wajen tabbatar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.



