A shirye-shiryen bukukuwan Easter masu zuwa, Babban Kwamandan Hukumar Tsaro da Kariya ta Farar Hula ta Najeriya (NSCDC), Farfesa Ahmed Abubakar Audi, ya amince da tura sama da jami’ai 57,000 a fadin kasar nan. Wannan gagarumin shiri, wanda ya hada da rundunonin musamman da jami’an leken asiri, na da nufin karfafa tsaron kasa da tabbatar da zaman lafiya a lokacin bukukuwan.
Shirin zai gudana a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya (FCT), a matsayin matakin kariya domin dakile duk wata barazana ga tsaro tare da tabbatar da kariyar Muhimman Kadarorin Kasa da Ababen More Rayuwa (CNAI).
Dangane da umarnin Babban Kwamandan, an umurci Kwamandojin Yankuna, Kwamandojin Jihohi, da Shugabannin Makarantu da su kula da tsare-tsaren tsaro a yankunansu. Wurare masu cunkoso kamar coci-coci, kasuwanni, wuraren shakatawa da sauran wuraren taruwar jama’a za su kasance karkashin tsauraran matakan sa ido, ta hanyar sintiri a fili da kuma ayyukan sirri domin dakile masu aikata laifi.
Farfesa Audi ya jaddada muhimmancin kara sanya ido da kuma hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro. Ya bayyana cewa musayar bayanan sirri cikin gaggawa da kuma daukar mataki cikin lokaci na da matukar muhimmanci ga nasarar wannan aiki.
“Burimmu shi ne tabbatar da zaman lafiya da tsaro a lokacin bukukuwan Easter,” in ji Babban Kwamandan. “Muna aiki kafada da kafada da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da doka da oda. Ina kuma kira ga iyaye da masu kula da yara da su kula da ‘ya’yansu yadda ya kamata, domin kada a yi amfani da su wajen tayar da hankalin jama’a.”
Haka kuma, rundunoni na musamman na hukumar, ciki har da CG’s Special Intelligence Squad (CG SIS), Mining Marshals, Special Female Squad (SFS), da Crack Squad, an sanya su cikin shirin ko-ta-kwana domin fuskantar duk wata barazana ga tsaron kasa.
Babban Kwamandan ya kuma bukaci al’umma da su kasance masu lura, su bayar da hadin kai ga hukumomin tsaro, tare da gaggauta kai rahoton duk wani abin da ake zargi ga ofishin NSCDC mafi kusa ko kowace hukuma ta tsaro.




