Ministan Tsaron Nijeriya, Christopher Gwabin Musa (Rtd), ya kai ziyararsa ta farko ta aiki zuwa Hedikwatar Rundunar Hadin Gwiwa ta Operation Fansan Yamma a Jihar Zamfara, inda ya jaddada sabon kudirin Gwamnatin Tarayya na ƙarfafa ayyukan tsaro a yankin Arewa maso Yamma.
Ministan ya samu tarba daga Kwamandan Rundunar Yanki, Manjo Janar W.B. Idris, tare da sauran manyan hafsoshin soja. Ziyarar ta ba shi damar duba yadda ake gudanar da ayyukan tsaro a filin daga, tattaunawa da shugabannin runduna, da kuma nazarin dabarun da ake amfani da su wajen yaƙar ta’addanci, fashi da makami da sauran miyagun laifuka a yankin.
Ziyarar ta zo ne bayan ƙaddamar da Motocin Yaƙi Masu Sulke (Armoured Personnel Carriers) da kuma Jirage Marasa Matuki (Unmanned Aerial Vehicles) da Gwamnatin Jihar Zamfara ta samar domin ƙarfafa ayyukan tsaro a yankin. Samar da waɗannan kayayyaki ya nuna haɗin kai tsakanin Gwamnatin Tarayya da ta Jiha wajen inganta tsaro.
Ana sa ran sabbin kayayyakin za su inganta motsin sojoji, tattara bayanan sirri, sa ido, bincike da kuma gaggauta mayar da martani kan barazanar ‘yan bindiga da sauran masu aikata laifuka. Jami’an soja sun bayyana cewa haɗa sabbin fasahohi cikin ayyukan tsaro zai ƙara inganta hangen nesa da kuma ingancin aiki.
Yayin da yake jawabi ga sojoji, Janar Musa ya sake tabbatar da aniyar Gwamnatin Tarayya na samar wa rundunonin soji kayan yaƙi na zamani domin tunkarar sabbin kalubalen tsaro. Ya yaba wa jami’ai da dakarun bisa jajircewarsu, ƙwazonsu da kuma ƙwarewarsu duk da wahalhalun aiki.
Ministan ya kuma ba da tabbacin ci gaba da samar da tallafin kayan aiki, inganta jin daɗin dakarun, da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomi domin ci gaba da samun nasara a yaƙi da rashin tsaro. Ya jaddada cewa dawo da zaman lafiya a Zamfara na da matuƙar muhimmanci ga tsaron ƙasa baki ɗaya.
A nasa jawabin, Kwamandan Rundunar Yanki, Manjo Janar Idris, ya gode wa Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Zamfara bisa goyon bayan da suke bayarwa. Ya ce sabbin kayayyaki da tallafin dabaru za su ƙara hanzarta ƙoƙarin rusa sansanonin ‘yan ta’adda da tabbatar da dorewar zaman lafiya, kwanciyar hankali da tsaro a Jihar Zamfara da ma yankin Arewa maso Yamma baki ɗaya.




