Babban Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, Olumode Samuel Adeyemi, I, a ranar Laraba, 4 ga Fabrairu 2026, ya mika Lambar Yabo ta Fitaccen Malami ga Mataimakin Sufritandan Kashe Gobara na II (ASF II), Ekene Isaac, a wajen liyafar cin abinci da Hukumar ta shirya a Makarantar Horaswa ta NDLEA Academy.
An ba da lambar yabon ne bisa la’akari da kwarewarsa ta musamman wajen koyarwa, jajircewarsa, da gagarumar gudummawar da ya bayar wajen nasarar kammala tsauraran horo na tsawon makonni tara ga Daliban Horaswa na Jami’an Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, Kashi na 06. Haka kuma, an karrama sauran malamai da suka yi fice a fannoni daban daban saboda jajircewarsu da kwarewarsu ta aiki.
Liyafar cin abincin ta bayar da kyakkyawan yanayi na tunani, godiya, da zumunci a tsakanin daliban horaswa da malamai, tare da karfafa al’adun Hukumar na bai wa cancanta muhimmanci da girmama nagarta. Wannan biki na daga cikin shirye shirye da ke gabanin Bikin Kammala Horaswa (Passing Out Parade), wanda zai gudana yau, yana nuna shigowar daliban a hukumance zuwa sabon mataki na rayuwarsu ta sana’a.





