An tsira daga harin da aka kai Yelwata a jihar Benue a watan Yunin shekarar 2025, Msurshima Apeh, ta bayyana irin mummunar azabar da ta sha yayin da ta yi jawabi a gaban Majalisar Dokokin Amurka, inda ta ce ta kalli yadda aka kashe dukkan ’ya’yanta biyar a gabanta.
Taron sauraron bayanan ya mayar da hankali ne kan matakin shugaban kasar Amurka Donald Trump na maido da Najeriya cikin jerin kasashen da ake kallon suna fama da cin zarafin addini.
Apeh ta bayyana yadda lamarin ya faru lokacin da ta ke ba da shaida ga kwamitin kula da harkokin Afirka na Majalisar Wakilai.
Ta ce, “Mun kwanta barci da karfe tara na dare, sai ga su Fulani tare da makamai sun auka mana a sansanin da muke kwana a Yelwata. An rufe mu a ciki, suka fara sare mutane da takubba kana kuma suna harbi.”
Ta ci gaba da cewa bayan sun gama kisa, sun zuba man fetur suka kunna wuta suka ƙone mutanen da dama a cikin gini.
Ta ce ta tsira ne bayan ta hango wani itace, ta yi maza ta haye ta ɓuya a sama, tana kallon yadda ake kashe yaranta.
“Yayinda ake wannan ta’asar, na hango itace sama na daga kaina. Na kama reshe na haye. A nan na samu damar ɓoyewa. A kasa kuma ’ya’yana biyar suna kuka, a gabana aka yi musu kisa,” in ji ta.
Apeh ta ce daga baya ta gudu cikin daji, inda masu ceto suka same ta suka fitar da ita, daga nan aka mayar da ita wani sabon sansani.
Harin Yelwata da ya faru a daren wata Yuni na 2025, an danganta shi ga wasu makiyaya masu dauke da makamai. Mutane da dama sun mutu, ciki har da fararen hula da jami’an tsaro guda biyar.
An kona gidaje da shaguna, tare da rasa dangi gaba ɗaya a wasu gidajen, ciki har da labarin da ya nuna an kashe mutane goma sha biyar a gida guda ɗaya.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya dakatar da wasu alkawura domin ya ziyarci jihar Benue, inda ya yi alƙawarin bincike da ɗaukar matakan magance matsalar.
A ziyarar tasa, ya gana da manyan shugabanni domin neman mafita mai ɗorewa, sannan ya ziyarci wadanda ke jinya a asibitoci.
Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya bayyana harin a matsayin barazana ga zaman lafiya da tsaron ƙasa, sannan ya ce za a tura karin jami’an tsaro domin kare rayuka da dukiya.
Ya kuma tabbatar da kama mutum ashirin da shida da ake zargi da hannu a harin Yelwata.
Hare haren sun jawo fushin jama’a a fadin Najeriya, inda shugabannin siyasa, kungiyoyin addini da kungiyoyin farar hula suka bukaci adalci da kuma daukar matakan tsaro masu karfi domin hana sake faruwar irin wannan mummunan hari.





