Kwamandan NSCDC Mining Marshals, ACC John Onoja Attah, Ya Samu Girmamawa a Matsayin Nation Builder Kan Yaki da Fasa-kaurin Ma’adinai

Kwamandan Rundunar NSCDC Special Mining Marshals, ACC John Onoja Attah, ya sake samun girmamawa a matakin ƙasa.

a wannan karon a matsayin “Nation Builder for Protection Against Illegal Mining” a bikin 3rd Nigeria’s Nation Builders Annual Awards da aka gudanar a Abuja.

A wurin Mining Marshals, wannan lambar yabo ba wai ado ba ne kawai. Shaidar ce ta jajircewa, sadaukarwa, da himmar da ACC Attah ke nunawa wajen jagorantar yaki da fasa-kaurin ma’adinai a fadin ƙasar nan.

An shirya taron ne ta hannun National Civil Society Coalition (NACCSO) tare da hadin gwiwar Vision-One Leadership Development Initiative, domin karrama mutanen da ayyukansu ke taimakawa wajen gina Najeriya mafi inganci da cigaba. Shugaban NACCSO, Emmanuel Johnny, ya yabawa ACC Attah kan “gwagwarmaya mai cike da jarumtaka da rashin gushewa” wajen kare dukiyar ma’adinai da a da ake wawashewa — ƙoƙarin da ya ce ya taimaka wajen “juyar da asarar kudaden shiga na Najeriya zuwa riba.”

A jawabinsa, ACC Attah ya mika wannan girmamawa ga Commandant General na NSCDC, Farfesa Abubakar Ahmed Audi, tare da gode wa Ministan Harkokin Cikin Gida, Dr. Olubunmi Tunji-Ojo, da Ministan Ma’adinai, Dr. Dele Alake, bisa goyon bayansu. Ya jaddada cewa aikinsu a bayyane yake: sanya bukatar kasa kafin ta kowa.

Sauran fitattun wadanda suka samu lambar yabo sun hada da:
• Janar C.G. Musa (rtd), tsohon CDS
• Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, Shugaban NECO
• Silas Agara, Darakta Janar na NDE
• CP Ifeanyi Henry Uche, Shugaban Police National Cybercrime Centre
• Hajiya Aisha Ahmed Audi, Shugabar CDOWA

Duk da yawan lambobin yabo da ake bayarwa a Abuja, wannan karramawar ta musamman ce ga Mining Marshals. Tana tabbatar da cewa karkashin jagorancin ACC John Onoja Attah, yaki da fasa-kaurin ma’adinai ba kawai ana gani ake yi ba yana canza tsarin wani bangare da a da aka san shi da isa da rashin bin doka.


  • Keji Mustapha

    Related Posts

    “Muna Tare da Ku”: Gwamna Zulum Ya Karfafa Guiwar Sojoji a Ziyara Damboa

    Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, a ranar Asabar ya yi jawabi ga sojojin rundunar 25 Task Force Brigade na Sojan Najeriya a Damboa, inda ya tabbatar da cikakken…

    “We Stand Firmly With You”: Governor Zulum Encourages Troops During Visit to Damboa

    Borno State Governor, Professor Babagana Umara Zulum, on Saturday addressed troops of the 25 Task Force Brigade of the Nigerian Army in Damboa, reaffirming the unwavering support of the state…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    “Muna Tare da Ku”: Gwamna Zulum Ya Karfafa Guiwar Sojoji a Ziyara Damboa

    “Muna Tare da Ku”: Gwamna Zulum Ya Karfafa Guiwar Sojoji a Ziyara Damboa

    “We Stand Firmly With You”: Governor Zulum Encourages Troops During Visit to Damboa

    “We Stand Firmly With You”: Governor Zulum Encourages Troops During Visit to Damboa

    NDLEA Ta Kama Kwayoyi Sama da Milyan 7.6 na Tramadol da Kilo 76,273 na Colorado da Skunk a Fadin Kasar

    NDLEA Ta Kama Kwayoyi Sama da Milyan 7.6 na Tramadol da Kilo 76,273 na Colorado da Skunk a Fadin Kasar

    NDLEA Seizes 7.6 Million Tramadol Pills, 76,273kg of Colorado and Skunk in Nationwide Raids…Destroys Major Drug Warehouses in Ekiti and Ondo Forests

    NDLEA Seizes 7.6 Million Tramadol Pills, 76,273kg of Colorado and Skunk in Nationwide Raids…Destroys Major Drug Warehouses in Ekiti and Ondo Forests

    Hedikwatar FFS Gombe Ta Karɓi Tawagar Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida Don Binciken Gamsuwar Jama’a na Kwata na 3 da na 4 (SERVICOM)

    Hedikwatar FFS Gombe Ta Karɓi Tawagar Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida Don Binciken Gamsuwar Jama’a na Kwata na 3 da na 4 (SERVICOM)

    FFS Gombe Command Hosts Interior Ministry Delegation for Q3 & Q4 SERVICOM Customer Satisfaction Assessment

    FFS Gombe Command Hosts Interior Ministry Delegation for Q3 & Q4 SERVICOM Customer Satisfaction Assessment