Zargin Shirya Juyin Mulki: Jami’an Tsaro Sun Yi Samame a Gidan Tsohon Minista Timipre Sylva a Abuja, Sun Kama Dan Uwansa

Rahotanni na baya-bayan nan sun nuna cewa jami’an Hukumar Leken Asiri ta Tsaro (Defence Intelligence Agency – DIA) sun kai samame a gidan tsohon Ministan Albarkatun Man Fetur, Cif Timipre Sylva, da ke Abuja, bisa zargin cewa yana da hannu a wani shirin juyin mulki. A yayin aikin, an ce sun kama dan uwansa mai suna Paga Sylva.

Majiyoyi sun bayyana cewa an kai samamen ne bayan samun bayanan sirri da suka danganta wasu ‘yan siyasa da zargin shirin tada zaune tsaye da nufin kawo cikas ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Wasu rahotanni da ba a tabbatar da su ba sun ce Sylva, wanda ya taba zama Gwamnan Jihar Bayelsa, ya gudu daga Najeriya ta cikin kogunan yankin Neja Delta zuwa Senegal, inda ake zargin yana shirin wucewa zuwa ƙasar Argentina, inda yake da wasu harkokin kasuwanci.

Wani majiyar cikin gida ya bayyana cewa ɗaya daga cikin jami’an soja da aka fara kama da zargin hannu a shirin juyin mulkin ya ambaci sunan tsohon Ministan yayin bincike. Haka kuma, an ce masu bincike sun gano kusan naira biliyan 46 a wani asusun da ake zargin yana da alaka da shi.

Rahotanni sun kuma nuna cewa jami’an tsaro sun kai samame a gidan Sylva da ke Bayelsa, inda aka ce sun gano tarin kuɗaɗe a kudi na kasashen waje tare da wasu muhimman takardu da ake zargin suna da nasaba da binciken.

A gefe guda, wasu rahotanni sun ce iyalan Al-Makura sun nemi taimakon malamai bayan kama ɗansu, wani Laftanar Kanal da ke bakin aiki, wanda shi ma ake zargin yana da alaka da binciken.

Haka kuma, wasu majiyoyi sun bayyana cewa Sylva ya nuna fushi bayan sake nasarar Gwamna Douye Diri a Bayelsa, inda ya zargi jam’iyyarsa ta APC da rashin “yin abin da ya dace” domin tabbatar da nasararsa.

A halin yanzu, babu wata sanarwa daga Hedkwatar Tsaro ko daga Sylva kansa game da wannan zargi.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    NSCDC Deploys Toma Enya as New Osun State Commandant

    By Samuel Ike. Abuja The Commandant-General of the Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC), Professor Ahmed Abubakar Audi, has approved the deployment of Commandant Toma Mathew Enya as the…

    Musa’s War of Words with El-Rufai: A Defence Minister on the Wrong Battlefield

    By Isiaka Mustapha, Editor-in-Chief, People’s Security Monitor Recent public comments by the Minister of Defence, General Christopher Musa (rtd.), against former Kaduna State Governor Nasir El-Rufai deserve serious scrutiny, particularly…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    NSCDC Deploys Toma Enya as New Osun State Commandant

    NSCDC Deploys Toma Enya as New Osun State Commandant

    Musa’s War of Words with El-Rufai: A Defence Minister on the Wrong Battlefield

    Musa’s War of Words with El-Rufai: A Defence Minister on the Wrong Battlefield

    DSS Under Ajayi: From Culture of Fear to Intelligence, Accountability and Rule of Law

    DSS Under Ajayi: From Culture of Fear to Intelligence, Accountability and Rule of Law

    NOUN Bursar Nasiru Marafa Reportedly Shot Dead in Zamfara

    NOUN Bursar Nasiru Marafa Reportedly Shot Dead in Zamfara

    Bauchi Senator Rejects Banditry Allegations, Calls Viral Videos Fabricated

    Bauchi Senator Rejects Banditry Allegations, Calls Viral Videos Fabricated

    SFU Investigates Multi-Billion Dollar Fraud Allegations in Nigeria’s Oil and Gas Sector

    SFU Investigates Multi-Billion Dollar Fraud Allegations in Nigeria’s Oil and Gas Sector