Sojojin Bataliya ta Musamman ta 198 da ke sansanin Forward Operating Base (FOB) Katarko ƙarƙashin Sashen 2 na Operation HADIN KAI (Arewa maso Gabas) sun yi nasarar dakile wani harin da ‘yan ta’addan Boko Haram suka kai da safe a ranar 23 ga Oktoba 2025.
Da misalin ƙarfe 03:05 na safe, ‘yan ta’addan sun yi ƙoƙarin shiga sansanin tare da amfani da manyan makamai. Amma jaruman sojojin sun nuna ƙwarewa, ƙarfin zuciya da jajircewa, inda suka yi amfani da ƙarfin wuta mai ƙarfi suka fatattaki maharan, suka yi musu babban rashi.
Bayan artabun, sojojin sun bi sawun ‘yan ta’addan har zuwa Gazargana, inda suka tilasta musu ja da baya cikin ruɗani tare da barin makamai da kayan su na yaki.
A yayin faɗan, babu wanda ya rasa ransa daga cikin sojojin, yayin da aka kashe ‘yan ta’adda 23, wasu kuma suka tsere da raunukan harbi. Kayan da aka kwato sun haɗa da bindigogi PKT guda 4, AK-47 guda 14, bututun RPG guda 1, bam ɗin RPG guda 2, bam ɗin morta 60mm guda 2, hand grenade guda 2, kayan IED guda 3, rediyo da aka lalata guda 1, da kuma harsasai iri daban-daban.
Bayan harin, Kwamandan Rundunar Sojojin Musamman ta 402, Birgediya Janar Mohammed Bako Shehu, ya kai ziyara FOB Katarko domin yaba wa sojojin bisa jarumta, jajircewa da kuma yadda suka nuna ƙwarewar yaki. Ya kuma isar da sakon jinjina daga Babban Hafsan Sojan Ƙasa (COAS), Kwamandan Rundunar Sojojin Musamman ta 4, da kuma Kwamandan Rundunar Dabaru (Theatre Commander). Ya ƙarfafa sojojin da su ci gaba da jajircewa, su kasance cikin shiri a koda yaushe, tare da tabbatar da cewa ba a bar ‘yan ta’addan da sararin yin abin da suke so ba.
A yayin ziyarar, Birgediya Janar Shehu ya ziyarci Asibitin Mataki na 2 (Level 2 Hospital) da ke Damaturu, inda ya duba wasu sojoji da suka samu ƙananan raunuka a wasu hare-hare na baya-bayan nan. Ya yaba musu bisa ƙarfin hali tare da tabbatar musu da cewa sojojin Najeriya za su ci gaba da tallafa musu har sai sun murmure gaba ɗaya.
Yanayin tsaro a yankin ya ci gaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali yayin da ƙwarin gwiwar sojojin ke daɗa ƙaruwa tare da ci gaba da gudanar da ayyukan tsabtace yankin daga ragowar ‘yan ta’adda.




