HUKUMAR KULA DA WUTA TA ƘASA (FFS) DA HUKUMAR SAYE DA SAYAR DA KAYAN GWAMNATI (BPP) SUN ƘARA ƘARFI A HADA KAI DOMIN INGANCI, TSABTAR AIKI DA TSARO A TSARIN SAYE DA SAYAR DA KAYAN GWAMNATI

Babban Kwamandan Hukumar Kula da Wuta ta Ƙasa (FFS), Olumode Samuel Adeyemi, ya jagoranci tawagar manyan jami’an hukumar a ziyarar ban girma ga Darakta Janar na Hukumar Saye da Sayar da Kayan Gwamnati (BPP), Dr. Adebimpe Adebowale Adedibu, a ofishin hukumar da ke Babban Birnin Kasuwanci (Central Business District), Abuja.

Manufar ziyarar ita ce ƙarfafa dangantakar aiki tsakanin hukumomin biyu da kuma zurfafa haɗin kai a fannin gaskiya, amana, da ingantaccen aiwatar da tsare-tsaren saye da sayar da kayan gwamnati.

A jawabin maraba da ya gabatar, Dr. Adedibu ya taya Babban Kwamandan murna bisa nadin sa, tare da yabawa irin jajircewar da ya nuna a lokacin da yake shugaban sashen saye a hukumar kula da wuta. Ya kuma jinjinawa hukumar bisa bin manufofin saye na gaskiya da daidaito, inda ya ambaci cewa nadin mace a matsayin mataimakiyar Babban Kwamanda na nuna cikakken kishin daidaito tsakanin maza da mata a cikin hukumar.

A martaninsa, Babban Kwamanda Adeyemi ya gode wa Darakta Janar bisa goyon baya da shawarwarin uba da yake ba hukumar. Ya bayyana cewa ziyarar na cikin matakan ƙarfafa haɗin kai tsakanin hukumomin biyu, musamman duba da muhimmancin rawar da BPP ke takawa wajen tabbatar da gaskiya da samun darajar kuɗin gwamnati.

Babban Kwamanda ya jaddada bukatar ƙara horar da jami’an saye da takardar ƙwararru domin ƙara ƙwarewa a fannin, tare da neman ƙarin damar horaswa ga jami’an FFS. Ya kuma bayyana cewa wasu ayyuka da aka fara shekaru da suka gabata sun tsaya saboda matsalolin kuɗi, inda ya roƙi BPP ta bayar da shawarwari kan yadda za a kammala su cikin tsari da kulawa.

A cikin shawarwarinsa, Babban Kwamanda Adeyemi ya ba da tayin cewa Hukumar Kula da Wuta za ta gudanar da atisayen tsaro da wayar da kan ma’aikata na BPP a kai a kai, kyauta ba tare da wani kuɗi ba. Ya kuma ba da shawarar a sanya takardar shaidar tsaro daga gobara a matsayin wani muhimmin sharadi kafin a amince da kowane aikin gwamnati, domin kare dukiyar gwamnati da rayukan jama’a.

A nasa jawabin, Dr. Adedibu ya yaba da irin ƙwarin guiwar Babban Kwamanda, yana mai cewa hukumar BPP ita ce “gogaggen matuki da ke jagorantar jirgin gwamnati zuwa sahun gaskiya da amana.” Ya tabbatar da cewa hukumar sa za ta ci gaba da aiki tare da FFS wajen horo, bin doka da kuma haɗa ƙa’idojin tsaro cikin tsarin saye na gwamnati.

Darakta Janar ya bayyana cewa hukumar BPP tana duba tsarin aikinta domin daidaitawa da zamani, tare da tabbatar da ci gaba da tallafawa hukumar kula da wuta bisa dokar Saye da Sayar da Kayan Gwamnati. Ya jaddada muhimmancin aiki tare da ƙwarewa tsakanin hukumomin gwamnati domin tabbatar da bin ka’ida da ingantaccen aiki.

Dr. Adedibu ya kuma amince da shirin Babban Kwamanda kan haɗa batun tsaro daga gobara cikin tsarin saye, inda ya sanar da cewa duk shirye-shiryen da BPP za ta gudanar daga yanzu za su haɗa da mintuna biyar zuwa goma na wayar da kai kan tsaro daga gobara, tare da la’akari da ƙara jerin binciken bin ƙa’idar FFS cikin ka’idojin da BPP ke amfani da su.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    Gombe Emerges Nigeria’s Most Secure State as Governor Inuwa Yahaya Receives National Security Leadership Award

    Pix: Gov. Yahaya Governor Muhammadu Inuwa Yahaya of Gombe State has been honoured with the prestigious 2026 Nigeria’s Most Secure State Excellence Award in recognition of his administration’s remarkable achievements…

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    The Management and Editorial Board of the People’s Security Monitor wishes to extend its profound and heartfelt appreciation to all distinguished guests, stakeholders, security leaders, partners, and participants who honoured…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gombe Emerges Nigeria’s Most Secure State as Governor Inuwa Yahaya Receives National Security Leadership Award

    Gombe Emerges Nigeria’s Most Secure State as Governor Inuwa Yahaya Receives National Security Leadership Award

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    2026 PSM SECURITY SUMMIT: OUR APPRECIATION

    2026 PSM SECURITY SUMMIT: OUR APPRECIATION

    People’s Security Monitor Confers 2026 Exceptional Leadership Award on Ondo NSCDC Commandant Ibiloye…Dedicates Award to Ondo NSCDC Personnel

    People’s Security Monitor Confers 2026 Exceptional Leadership Award on Ondo NSCDC Commandant Ibiloye…Dedicates Award to Ondo NSCDC Personnel

    BREAKING: EMIR OF ARGUNGU CALLS FOR LEGAL COMMUNITY SELF-PROTECTION MEASURES AGAINST BANDITRY

    BREAKING: EMIR OF ARGUNGU CALLS FOR LEGAL COMMUNITY SELF-PROTECTION MEASURES AGAINST BANDITRY

    ONDO NSCDC Commandant Earns National Recognition for Exceptional Leadership in Civil Defence Operations

    ONDO NSCDC Commandant Earns National Recognition for Exceptional Leadership in Civil Defence Operations