A ranar Litinin, harkokin tattalin arziki da zamantakewa a Babban Birnin Tarayya (FCT) sun tsaya cik bayan da masu zanga-zangar neman a saki shugaban ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, ba tare da sharadi ba suka fito ƙarƙashin jagorancin ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowore.
Zanga-zangar, wadda aka fara tun da karfe 6:00 na safe, ta gamu da tsauraran matakan tsaro inda ‘yan sanda suka toshe manyan hanyoyin shiga Abuja, lamarin da ya haddasa cunkoso mai tsanani da ya hana ma’aikata zuwa wuraren aikinsu.
An shirya gangamin a matsayin zanga-zangar lumana, amma daga bisani ya rikide zuwa tashin hankali a yankin Maitama lokacin da jami’an tsaro suka yi amfani da hayaki mai kwalla don tarwatsa masu zanga-zanga. Shaidun gani da ido sun ce masu zanga-zangar sun taru a kusa da ofishin hukumar sadarwa ta ƙasa (NCC), suna rera taken “Free Nnamdi Kanu Now”, kafin a ji karar harbi da mutane suka fara gudu.
Tun a ranar Lahadi, rundunar ‘yan sanda ta gargadi masu zanga-zanga da kada su kusanci fadar shugaban kasa, majalisar dokoki, da sauran muhimman wurare, tare da barazanar ɗaukar mataki idan aka karya doka.
Hanyoyi Sun Rufe, Fasinjoji Sun Makale
Toshe hanyoyi da jami’an tsaro suka yi ya jefa mazauna birnin da masu tafiya aiki cikin wahala. Mota daga yankuna kamar Bwari, Ushafa, Dutse, da Kubwa sun fuskanci cunkoso mafi tsanani, yayin da hanyoyin Nyanya–Mararaba da Keffi–Abuja suka cika da dogayen layuka sakamakon binciken sojoji a kusa da gadar Karu.
Wani direba a yankin Sokale, Usman Jibrin, ya koka da cewa:
“Na makale a wuri ɗaya sama da awa ɗaya. Idan mutane suna son zuwa Villa, me ya sa za a hukunta mu da muke nesa da can? Wannan rashin adalci ne.”
Saboda shirin masu zanga-zanga na kai farmaki zuwa fadar shugaban kasa, jami’an tsaro sun kulle dukkan hanyoyin shiga Aso Villa, suka ƙara bincike, har ma suka hana wasu ma’aikatan Villa shiga ta hanyar da suka saba bi.
Kama, Duka, da Lalata Kayan Aiki
Jami’an tsaro sun kama wasu daga cikin masu zanga-zangar ciki har da lauya na Nnamdi Kanu, Mista Aloy Ejimakor, da ƙaninsa Fineboy Kanu. Rahotanni sun nuna cewa Sowore ya tsere daga kama.
Wasu ‘yan jarida da ke ruwaito lamarin suma sun gamu da cin zarafi. Wani ɗan jaridar AFP, John Okunyomih, ya ce jami’an tsaro sun mare shi tare da lalata kamarar aikinsa. Haka kuma, ɗan jaridar Business Day, Tony Ailemen, ya ce jami’an ‘yan sanda sun harba hayaki kai tsaye zuwa cikin motarsa, wanda ya fashe gilashin baya.
Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya (NUJ) reshen FCT ta yi Allah-wadai da harin da aka kai wa ‘yan jarida, tana kiran hakan “sabon hari ga ‘yancin kafafen yada labarai.” NUJ ta bukaci babban sifeton ‘yan sanda da kwamishinan FCT su binciki lamarin, su hukunta jami’an da suka aikata hakan, kuma su biya diyyar kayan da aka lalata.
Sowore Ya Yi Barazanar Zanga-Zangar Cigaba
Da yake mayar da martani, Omoyele Sowore ya bukaci a saki waɗanda aka kama nan da nan, yana kiran tsare su “ba bisa doka ba.”
A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin X (tsohon Twitter), Sowore ya gargadi rundunar ‘yan sanda ta FCT cewa idan ba su saki Barrister Aloy Ejimakor, Fineboy Kanu, da sauran masu zanga-zanga ba, za su gudanar da mamaya zuwa hedkwatar ‘yan sanda ta FCT.




