SABON KONTROLA NA JIHAR RIVERS, ACF OBASI IKENNA, YA KARƁI RAGAMA A HUKUMAR KULA DA WUTA TA ƘASA (FEDERAL FIRE SERVICE)

Hukumar Kula da Wuta ta Ƙasa, Sashen Jihar Rivers, ta gudanar da bikin mika mulki a ranar Laraba, 15 ga Oktoba, 2025, inda tsohuwar Kontrola ta Jiha, ACF Hawa Weli, ta mika ragamar mulki ga sabon da aka nada, ACF Obasi Ikenna.

An gudanar da wannan muhimmiyar bukin a Hedikwatar Hukumar da ke Port Harcourt, wanda ke nuna sauyin shugabanci cikin lumana da nufin tabbatar da ci gaba da ingantaccen aiki da kuma ƙarfafa jajircewar Hukumar wajen kare rayuka da dukiyoyi daga gobara a faɗin jihar.

A cikin jawabin bankwana, ACF Hawa Weli ta gode wa shugabanci da jami’an hukumar bisa goyon baya da hadin kai da suka nuna a lokacin aikinta, tare da kira gare su da su ci gaba da nuna irin wannan kishin da haɗin kai ga sabon Kontrola.

Shi kuwa sabon Kontrola na Jiha, ACF Obasi Ikenna, a jawabinsa na farko, ya gode wa Babban Kontrola Janar na Hukumar, Dakta Olumide Samuel Adeyemi, bisa amincewar da ya nuna gare shi da kuma damar da aka ba shi na yi wa ƙasa hidima. Ya yi alkawarin gina kan nasarorin da wanda ya gabace shi ya samu tare da ƙara ƙarfafa hanyoyin rigakafi da martani cikin gaggawa ga matsalolin gobara a Jihar Rivers.

An halarci bukin mika mulkin ne da jami’ai da ma’aikatan Hukumar, waɗanda suka bayyana shirinsu na mara baya ga sabon shugabanci domin cika manufofin Hukumar.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    The Management and Editorial Board of the People’s Security Monitor wishes to extend its profound and heartfelt appreciation to all distinguished guests, stakeholders, security leaders, partners, and participants who honoured…

    2026 PSM SECURITY SUMMIT: OUR APPRECIATION

    The Management and Editorial Board of the People’s Security Monitor will like to extend its profound and heartfelt appreciation to all distinguished guests, stakeholders, security leaders, partners, and participants who…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    2026 PSM SECURITY SUMMIT: OUR APPRECIATION

    2026 PSM SECURITY SUMMIT: OUR APPRECIATION

    People’s Security Monitor Confers 2026 Exceptional Leadership Award on Ondo NSCDC Commandant Ibiloye…Dedicates Award to Ondo NSCDC Personnel

    People’s Security Monitor Confers 2026 Exceptional Leadership Award on Ondo NSCDC Commandant Ibiloye…Dedicates Award to Ondo NSCDC Personnel

    BREAKING: EMIR OF ARGUNGU CALLS FOR LEGAL COMMUNITY SELF-PROTECTION MEASURES AGAINST BANDITRY

    BREAKING: EMIR OF ARGUNGU CALLS FOR LEGAL COMMUNITY SELF-PROTECTION MEASURES AGAINST BANDITRY

    ONDO NSCDC Commandant Earns National Recognition for Exceptional Leadership in Civil Defence Operations

    ONDO NSCDC Commandant Earns National Recognition for Exceptional Leadership in Civil Defence Operations

    FEDERAL FIRE SERVICE KWARA COMMAND HOSTS AL-WAHYAIN INTERNATIONAL ACADEMY STUDENTS ON FIRE SAFETY EDUCATIONAL EXCURSION

    FEDERAL FIRE SERVICE KWARA COMMAND HOSTS AL-WAHYAIN INTERNATIONAL ACADEMY STUDENTS ON FIRE SAFETY EDUCATIONAL EXCURSION