Kwamandan Jihar Legas Ya Karrama Jami’ai Mafi Fice, Ya Kuma Ja Hankalinsu Kan Gaskiya da Kwarewa a Aiki

Kwamandan Hukumar Tsaro da Kare Fararen Hula ta Ƙasa (NSCDC) na Jihar Legas, Mista Keshinro Adedotun, ya karrama jami’ai goma (10) da suka nuna bajinta a cikin horo da sake horarwa da aka gudanar a Kwalejin Kula da Tsaro da ke Oke-Mosan, Abeokuta, Jihar Ogun.

An gudanar da bikin karramawar ne yayin taron muster parade da aka shirya a Hedikwatar Hukumar da ke Alausa, Ikeja, a ranar Talata, 14 ga Oktoba, 2025, inda Kwamandan ya karɓi sabbin jami’an da aka horar da kuma sake horarwa, guda dari biyu da saba’in da huɗu (274). Jami’an sun halarci shirye-shiryen ƙwarewa na COCATRAP, FOAHT, da Agro Rangers da aka gudanar tsakanin watan Mayu zuwa Oktoba, 2025, ga rukuni na A, B, da C.

Yayin da yake jawabi, Kwamandan Adedotun ya yaba wa jajircewa da himmar jami’an a lokacin horon, yana mai kira gare su da su ci gaba da aiki cikin kwarewa, gaskiya da bin ƙa’ida. Ya tunatar da su cewa halayensu da yadda suke gudanar da aiki na wakiltar martabar hukumar, don haka ya shawarce su da su kasance jakadu nagari na NSCDC a duk inda suke aiki.

A matsayin lada da yabo, Kwamandan ya ba wa jami’ai goma (10) da suka fi kowa fice a lokacin horo kyautar kuɗi, yana mai bayyana nasararsu a matsayin sakamakon jajircewa, daidaito da sadaukarwa.

Ya kuma tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da mayar da hankali kan inganta ƙwarewa da horar da jami’anta, yana mai jaddada cewa ci gaba da horo da sake horarwa na da matuƙar muhimmanci wajen ƙara ingancin aiki da tabbatar da tsaron ƙasa.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    Nigeria, UK Strengthen Security Alliance to Tackle Terrorism, Cybercrime and Maritime Threats

    By Tunji Braimoh, Abuja Nigeria and the United Kingdom have renewed their commitment to expanding security and defence cooperation, agreeing on a broad framework to address terrorism, cybercrime, maritime insecurity,…

    FCT Police Name Four Officers Accused of Extorting ₦52,000 From ICPC Chairman

    By Tunji Braimoh, Abuja The Federal Capital Territory (FCT) Police Command has identified four police officers arrested and detained for allegedly extorting ₦52,000 from the Chairman of the Independent Corrupt…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Nigeria, UK Strengthen Security Alliance to Tackle Terrorism, Cybercrime and Maritime Threats

    Nigeria, UK Strengthen Security Alliance to Tackle Terrorism, Cybercrime and Maritime Threats

    FCT Police Name Four Officers Accused of Extorting ₦52,000 From ICPC Chairman

    FCT Police Name Four Officers Accused of Extorting ₦52,000 From ICPC Chairman

    DSS Challenges Life Sentences, Pushes for Execution of Ansaru Commanders

    DSS Challenges Life Sentences, Pushes for Execution of Ansaru Commanders

    Defence Ministry Debunks Claims of Minister’s Resignation, Describes Report as False

    Defence Ministry Debunks Claims of Minister’s Resignation, Describes Report as False

    Sokoto Government Donates Vehicles, Motorcycles to Boost NSCDC Operations

    Sokoto Government Donates Vehicles, Motorcycles to Boost NSCDC Operations

    Nigerian Army Disowns Fake Recruitment Advert, Warns Nigerians Against Fraudsters

    Nigerian Army Disowns Fake Recruitment Advert, Warns Nigerians Against Fraudsters