Olumode Ya Kaddamar da Kwamitin Musamman na Binciken Gine-ginen Jama’a da Masu Zaman Kansu Domin Ƙarfafa Tsaron Wuta

Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Wuta ta Ƙasa (Federal Fire Service (FFS), Olumode Adeyemi Samuel, ya kaddamar da Kwamitin Musamman na Binciken Gine-ginen Jama’a da Masu Zaman Kansu, a wani mataki na ƙarfafa bin ƙa’idodin tsaron wuta da kuma inganta ɗorewar tsaron ƙasa.

An gudanar da bikin kaddamarwar ne a Hedikwatar Hukumar da ke Abuja, ƙarƙashin taken “Ƙarfafa Bin Dokokin Tsaron Wuta a Gine-ginen Jama’a: Kira zuwa Aiki Domin Ɗorewar Tsaron Ƙasa.” Wannan mataki ya nuna sabon himmar Hukumar wajen rage haɗarin gobara da kuma hana afkuwar manyan bala’o’i da za a iya guje musu.

Yayin jawabinsa, Shugaban Hukumar ya nuna damuwa kan yawaitar gobara a manyan birane kamar gobarar Afritower da ta tashi a Legas da kuma gobarar wasu manyan shaguna a Abuja, yana mai cewa hakan ya nuna buƙatar tsaurara doka kan bin ƙa’idodin tsaron wuta.

Olumode ya bayyana cewa sabon kwamitin da aka kafa zai yi taswirar gine-ginen jama’a a faɗin ƙasar, ya tantance matakin haɗarin gobara a kowanne, ya gudanar da bincike kan yadda ake bin ƙa’idodin tsaro, sannan ya gabatar da shawarwari ga hukumar don jagorantar matakan aiwatar da doka da tsare-tsaren gwamnati.

Ya sake jaddada aniyar Hukumar wajen kare rayuka, dukiyoyi da muhimman kadarorin ƙasa, yana mai cewa “tsaron wuta ba zaɓi ba ne, wajibi ne ga kowa da kowa.”

Kwamitin, wanda Mataimakin Shugaban Hukumar (ACG) Bolarinde Tajudeen Muhammed, Shugaban Sashen Bincike, Tsanantawa da Aiwan Doka ke jagoranta, ya ƙunshi manyan jami’ai ciki har da Mataimakin Shugaban Ayyuka na Babban Birnin Tarayya (FCT), Provost Marshal, Jami’in Hulɗa da Jama’a na Ƙasa, da Daraktan Shari’a wanda shi ne Sakatare.

Yayin da yake kaddamar da kwamitin, Shugaban Hukumar ya bukaci mambobin su gudanar da aikinsu da ƙwarewa, gaskiya da cikakken sadaukarwa ga manufar hukumar ta kare gine-gine da wuraren zama daga haɗarin gobara. Haka kuma ya roƙi masu gine-gine, manajojin shaguna da masu mallakar kadarori su ba da cikakken haɗin kai yayin aikin binciken, yana mai tabbatar da cewa aikin an shirya shi ne domin kare rayuka da kuma inganta tsarin tsaron jama’a a ƙasar nan.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    Nigeria, UK Strengthen Security Alliance to Tackle Terrorism, Cybercrime and Maritime Threats

    By Tunji Braimoh, Abuja Nigeria and the United Kingdom have renewed their commitment to expanding security and defence cooperation, agreeing on a broad framework to address terrorism, cybercrime, maritime insecurity,…

    FCT Police Name Four Officers Accused of Extorting ₦52,000 From ICPC Chairman

    By Tunji Braimoh, Abuja The Federal Capital Territory (FCT) Police Command has identified four police officers arrested and detained for allegedly extorting ₦52,000 from the Chairman of the Independent Corrupt…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Nigeria, UK Strengthen Security Alliance to Tackle Terrorism, Cybercrime and Maritime Threats

    Nigeria, UK Strengthen Security Alliance to Tackle Terrorism, Cybercrime and Maritime Threats

    FCT Police Name Four Officers Accused of Extorting ₦52,000 From ICPC Chairman

    FCT Police Name Four Officers Accused of Extorting ₦52,000 From ICPC Chairman

    DSS Challenges Life Sentences, Pushes for Execution of Ansaru Commanders

    DSS Challenges Life Sentences, Pushes for Execution of Ansaru Commanders

    Defence Ministry Debunks Claims of Minister’s Resignation, Describes Report as False

    Defence Ministry Debunks Claims of Minister’s Resignation, Describes Report as False

    Sokoto Government Donates Vehicles, Motorcycles to Boost NSCDC Operations

    Sokoto Government Donates Vehicles, Motorcycles to Boost NSCDC Operations

    Nigerian Army Disowns Fake Recruitment Advert, Warns Nigerians Against Fraudsters

    Nigerian Army Disowns Fake Recruitment Advert, Warns Nigerians Against Fraudsters