Ministan Cikin Gida Ya Karrama Sabbin Mataimakan Babban Kwamandan NSCDC, Ya Bukace Su Da Shugabanci Nagari Da Himma Wajen Tsaron Kasa

Ministan Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya karrama sabbin Mataimakan Babban Kwamandan (DCG) guda uku na Hukumar Tsaro da Kare Muhimman Abubuwa ta Kasa (NSCDC), inda ya jaddada musu muhimmancin shugabanci na gaskiya, ladabi, da sabuwar jajircewa ga tsaron kasa.

A yayin bikin, Ministan ya bayyana cewa daukakar mukaman ta fito ne bisa cancanta, shekaru a aiki, da adalci, yana mai cewa wannan karin matsayi na nuni da nauyin sabis da sadaukarwa ga ‘yan Najeriya.

“Ba wai sabon alamar mukami kawai kuke sanya ba, ku na ɗaukar sabbin alhakai ne,” in ji shi. “Ku shugabanci da misali, ku rika koya wa wadanda ke biyowa bayanku, ku kuma nuna shugabanci na aminci, tausayi, da jarumta. Dole ne ‘yan kasa su ji tasirin aikin ku ta hanyar tsaro, kare rayuka, da kiyaye muhimman kadarorin kasa.”

Ya kuma tabbatar musu da goyon bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu wajen jin dadin su, ci gaba da gyare-gyare, da kawo karshen tsaikon mukamai a hukumar, yana mai cewa nasarar hukumar na da alaka kai tsaye da samun al’umma masu aminci a fadin kasar.

A cikin sakon sa na fatan alheri, Babban Kwamandan NSCDC, Farfesa Ahmed Abubakar Audi, ya taya sabbin DCG din murna tare da bukatar su tabbatar da amincewar da aka nuna musu ta hanyar kara dagewa wajen aiwatar da aikin hukumar. “Wannan karin girma ba na ku kadai bane; na miliyoyin ‘yan Najeriya ne da ke dogaro da hukumar don tsaro da fata,” in ji shi.

Wadanda aka karrama da matsayin Mataimakan Babban Kwamandan sun hada da: DCG Abdulkadir Sulu, DCG Abiakam-Omanu Christiana, da DCG Bridget Taylor.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    Commandant Chinedu Revamps Female Squad, Flags Off School Protection Patrols

    …Squad Begins Statewide School Visits, Enforces Park Regulations in Asaba… In line with the operational activities rolled out by the Delta State Commandant of the Nigeria Security and Civil Defence…

    psm

    Share on Facebook Post on X Follow us

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Commandant Chinedu Revamps Female Squad, Flags Off School Protection Patrols

    Commandant Chinedu Revamps Female Squad, Flags Off School Protection Patrols

    psm

    5 Cybersecurity Predictions for 2026

    5 Cybersecurity Predictions for 2026

    How to Ensure Security Barriers Don’t Become Guest Barriers

    How to Ensure Security Barriers Don’t Become Guest Barriers

    VGN Commander General, Navy Captain Umar Bakori (rtd) to Speak on “Community Driven Security: A Key Pillar for a Safer Nation” at 2025 People’s Security Monitor Security Summit

    VGN Commander General, Navy Captain Umar Bakori (rtd) to Speak on “Community Driven Security: A Key Pillar for a Safer Nation” at 2025 People’s Security Monitor Security Summit

    NSCDC Special Mining Marshal Czar, John Onoja Attah, to Speak on “Economic Benefits of a Sustainable and Responsible Mining Industry” at 2025 People’s Security Monitor Security Summit

    NSCDC Special Mining Marshal Czar, John Onoja Attah, to Speak on “Economic Benefits of a Sustainable and Responsible Mining Industry” at 2025 People’s Security Monitor Security Summit