Rundunar ’Yan sandan Najeriya ta ceto ragowar matafiya 13 da aka sace a kan hanyar Makurdi–Otukpo a jihar Benue, ciki har da dalibai takwas da ke shirin rubuta jarabawar Hukumar Shiga Jami’o’i da Shirin Matriculation (JAMB).
An kubutar da wadanda abin ya shafa ne a yayin wani hadin gwiwar aikin bincike da ceto da aka gudanar da sanyin safiyar ranar Lahadi a wani daji da ke yankin Okete Ward a karamar hukumar Ohimini.
Wadanda aka ceto sun hada da Hycent Oko mai shekaru 56; Elaiguli Joshua, 25; Orili Raphael, 29; Sunday Augustine, 18; Emmanuel Elaicha, 21; Gbile Nguyor Daniel, 18; Ukacha Tersoo, 18; da Nyikwagh Aoridakator, 22.
Sauran sun hada da Iornav Ngukuhan, 18; Nyikwagh Benjamin, 18; Buker Agatha, 19; Paul Wende, 29; da Akor Jessica, 19.
Dukkanin wadanda aka ceto an kwashe su zuwa Babban Asibitin Otukpo, inda suke karbar magani kan raunukan da suka samu yayin tsare su.




