Jami’an Rundunar Mayakan Hakar Ma’adanai ta Hukumar Tsaron Fararen Hula ta Najeriya (NSCDC) sun gudanar da wani gagarumin samame a garin Saki, Jihar Oyo, inda suka tarwatsa ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba tare da korar masu aikata hakan.
Wannan samame na cikin wani shiri na kasa baki ɗaya da Rundunar ke aiwatarwa domin tsabtace bangaren hakar ma’adanai, kare dukiyar ma’adanai ta ƙasa, da kuma tabbatar da bin ka’idoji a yankunan hakar ma’adanai.
Da yake magana a madadin Babban Kwamandan NSCDC, Ahmed Abubakar Audi, Kwamandan da ke jagorantar rundunar, Mataimakin Kwamandan Korp (ACC) John Onoja Attah, ya yabawa jami’an Mayakan Hakar Ma’adanai bisa kwarewa, da’a, da jajircewarsu wajen aiwatar da aiki.
ACC Attah ya jaddada kudirin Rundunar na ci gaba da kakaba matakan doka kan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a fadin kasar nan, yana mai cewa ba za a dakatar da wannan yaki ba har sai an samu cikakken bin dokoki da ka’idojin hakar ma’adanai.
Ya kara da cewa goyon bayan da shugabancin NSCDC ke bayarwa na kara wa jami’an kwarin gwiwa wajen gudanar da ayyukansu, tare da tabbatar da cewa Rundunar za ta ci gaba da kare hakar ma’adanai bisa doka, cikin tsaro, da kuma kare muhalli.
Rundunar NSCDC ta gargadi masu aikata hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba cewa za a kama su tare da gurfanar da su gaban kotu bisa ga dokokin da suka dace, yayin da ake ci gaba da ayyukan sintiri da samame a fadin kasar nan.



