Kokarin Najeriya na dakile harkar hakar ma’adinai ba bisa doka ba da kuma kare muhimman albarkatun kasa ya samu babban goyon baya, yayin da Ofishin MDD Kan Magunguna da Laifuka (UNODC) ya fara wani shirin horar da Ma’aikatan Mining Marshals na Hukumar NSCDC don kara musu kwarewa.
Shirin horon, wanda kasar Canada ta dauki nauyin aiwatarwa a karkashin aikin Strengthening Nigeria’s Response to Criminal and Terrorist Finance Related to Minerals, an tsara shi ne domin kara wa jami’an Mining Marshals dabarar gano, bincike da kuma katse hanyoyin kudaden haram da ke da alaka da hakar ma’adinai da kungiyoyin ta’addanci ke amfana da su.
An tsara gudanar da taron ne daga 25 zuwa 28 ga Nuwamba 2025 a Abuja. Taron zai kara zurfafa kwarewar wasu zababbun jami’an NSCDC wajen yaki da zirga-zirgar kudaden haram da ke fitowa daga hakar ma’adinai ba bisa doka ba, hada-hadar kudin kungiyoyin ta’addanci da kuma safarar kudi a bangaren ma’adinai. Haka kuma, shirin zai karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi daban-daban da ke kula da tsaron albarkatun kasa.
UNODC ta nemi a turo mata jami’ai 20 masu kwarewar fasaha, ciki har da jami’in hada-hada, musamman wadanda suke da gogewa a fannin yaki da hakar ma’adinai ba bisa doka ba da kuma laifukan kudi da suka shafi hakar ma’adinai.
Yayin bude taron, Babban Kwamandan NSCDC, Farfesa Abubakar Ahmed Audi (mni, OFR), ya yabawa wannan hadin gwiwa da UNODC, yana mai kiran shi “muhimmin aikin hadin kan kasa da kasa domin kare albarkatun ma’adinai na Najeriya daga satar albarkatu da tsoma bakin miyagu.” ACG Muktar Lawal ne ya wakilce shi, inda ya tabbatar da cewa hukumar za ta ba da cikakken goyon baya ga wannan shiri, wanda ya dace da manufar gwamnati na kare albarkatun kasa.
Shugaban Mining Marshals Corps, John Onoja Attah, ya ce wannan gudunmuwa daga UNODC na nuna kudirin gwamnati na tsaftace bangaren ma’adinai. Ya kara da cewa jami’ansa za su ci gaba da aiki bisa tsari, ladabi da jajircewa wajen aiwatar da doka.
Masu ruwa da tsaki sun jaddada cewa yadda harkar hakar ma’adinai ba bisa doka ba ke kara rikitarwa ya nuna bukatar karin ilimin fasaha da sabbin kayan bincike. Wannan horo daga UNODC zai koyar da Mining Marshals dabarun tattara bayanan leken asiri, nazarin bayanai da kuma bibiyar kudaden da ke shiga harkokin haramtacciyar hakar ma’adinai.
Bugu da kari, taron zai ba da dama ga mahalarta su sake nazarin dabarun aiki a fagen aiki, hulda da al’umma da kuma gaggawar daukar mataki. Wannan zai tabbatar da cewa bayanan da ake tattarawa daga kasa suna tallafawa aikin bincike da kama masu laifi a wuraren hakar ma’adinai.
Yayin da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba ke haifar da asarar kudaden shiga, tabarbarewar tsaro, lalacewar muhalli da kuma kashe-kashen kungiyoyin ta’addanci, hadin gwiwar UNODC da NSCDC na zama babban mataki wajen inganta karfin Najeriya na kare dukiyar kasa da lalata tattalin arzikin haramtattun ma’adinai. Ana sa ran taron zai zama sabon matakin ci gaba wajen samar da tsari mai karfi na kare ma’adinai a fadin kasar.





