Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya sake caccakar Gwamnatin Tarayyar Najeriya kan abin da ya kira yawan hare-hare da cin zarafin da ake yi wa Kiristoci a sassan ƙasar.
Trump ya yi wannan furuci ne a cikin wani sautin hira da aka watsa a shirin The Brian Kilmeade Show na Fox News Radio a ranar Juma’a, inda ya zargi gwamnatin Najeriya da sakaci wajen magance tashin hankalin da ke ƙaruwa.
A cewar sa, idan gwamnatin Najeriya ta ci gaba da kasa ɗaukar mataki, Amurka na iya dakatar da tallafin kuɗi da take bawa Najeriya.
“Ina ganin Najeriya abin kunya ce. Gaba ɗaya abin kunya ne. Ana kashe mutane a dubban. Wannan kisan kare-dangi ne, kuma ina matuƙar fusata da hakan,” in ji Trump.
Ya kara da cewa gwamnatin Najeriya ta gaza magance hare-haren.
“Mu muna biyan su tallafi mai yawa. Za mu iya dakatar da shi. Gwamnatin ba ta yin komai. Sun gaza. Ana kashe Kiristoci babu kakkautawa. Ku sani, har zuwa makonni biyun da suka gabata da na shiga cikin lamarin, babu wanda ma yake magana akai,” ya ce.
A baya-bayan nan, Trump ya ayyana Najeriya a matsayin Ƙasar da ke cikin Babban Barazana saboda zargin kisan Kiristoci, yana mai cewa addinin Kirista na fuskantar “barazana ga wanzuwarsa” a Najeriya.
Ya gargadi cewa idan gwamnatin Najeriya ta kasa dakatar da kisan jama’a, martanin Amurka zai kasance “mai sauri, mai ƙarfi, kuma mai ɗaci.”
Wannan furuci nasa ya haifar da ƙarin damuwa a fannin diflomasiyya, lamarin da ya sa gwamnatin Najeriya ta tura tawaga ta musamman zuwa Amurka domin tattaunawa.
A ranar Alhamis, Mai Bada Shawara kan Tsaron Kasa, Nuhu Ribadu, ya jagoranci tawagar Najeriya wajen ganawa da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, a Pentagon. A cewar Pentagon, Hegseth ya bukaci Najeriya ta ɗauki matakai masu ƙarfi domin dakile hare-hare da ke ƙara ta’azzara musamman kan al’ummomin Kirista.
Haka kuma, a daren Laraba a birnin Washington DC, Ɗan Majalisar Dokokin Amurka, Riley Moore, ya gana da tawagar Najeriya. Ya bayyana tattaunawar su kan yaki da ta’addanci da kare al’ummomin da ke cikin haɗari a matsayin “gaskiya, bayyananna, kuma mai amfani.”
Mambobin tawagar Najeriya sun haɗa da:
– Bianca Ojukwu, Karamin Ministan Harkokin Waje
– Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Egbetokun
– Babban Lauyan Tarayya, Lateef Fagbemi (SAN)
– Shugaban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Olatunbosun Oluyede
– Daraktan Leken Asiri na Tsaro, Laftanar Janar Emmanuel Undiendeye



