Trump Ya Zargi Gwamnatin Najeriya da Rashin Dakile Kisan Jama’a, Ya Yi Barazanar Dakatar da Tallafin Amurka

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya sake caccakar Gwamnatin Tarayyar Najeriya kan abin da ya kira yawan hare-hare da cin zarafin da ake yi wa Kiristoci a sassan ƙasar.

Trump ya yi wannan furuci ne a cikin wani sautin hira da aka watsa a shirin The Brian Kilmeade Show na Fox News Radio a ranar Juma’a, inda ya zargi gwamnatin Najeriya da sakaci wajen magance tashin hankalin da ke ƙaruwa.

A cewar sa, idan gwamnatin Najeriya ta ci gaba da kasa ɗaukar mataki, Amurka na iya dakatar da tallafin kuɗi da take bawa Najeriya.

“Ina ganin Najeriya abin kunya ce. Gaba ɗaya abin kunya ne. Ana kashe mutane a dubban. Wannan kisan kare-dangi ne, kuma ina matuƙar fusata da hakan,” in ji Trump.

Ya kara da cewa gwamnatin Najeriya ta gaza magance hare-haren.

“Mu muna biyan su tallafi mai yawa. Za mu iya dakatar da shi. Gwamnatin ba ta yin komai. Sun gaza. Ana kashe Kiristoci babu kakkautawa. Ku sani, har zuwa makonni biyun da suka gabata da na shiga cikin lamarin, babu wanda ma yake magana akai,” ya ce.

A baya-bayan nan, Trump ya ayyana Najeriya a matsayin Ƙasar da ke cikin Babban Barazana saboda zargin kisan Kiristoci, yana mai cewa addinin Kirista na fuskantar “barazana ga wanzuwarsa” a Najeriya.

Ya gargadi cewa idan gwamnatin Najeriya ta kasa dakatar da kisan jama’a, martanin Amurka zai kasance “mai sauri, mai ƙarfi, kuma mai ɗaci.”

Wannan furuci nasa ya haifar da ƙarin damuwa a fannin diflomasiyya, lamarin da ya sa gwamnatin Najeriya ta tura tawaga ta musamman zuwa Amurka domin tattaunawa.

A ranar Alhamis, Mai Bada Shawara kan Tsaron Kasa, Nuhu Ribadu, ya jagoranci tawagar Najeriya wajen ganawa da Sakataren Tsaron Amurka, Pete Hegseth, a Pentagon. A cewar Pentagon, Hegseth ya bukaci Najeriya ta ɗauki matakai masu ƙarfi domin dakile hare-hare da ke ƙara ta’azzara musamman kan al’ummomin Kirista.

Haka kuma, a daren Laraba a birnin Washington DC, Ɗan Majalisar Dokokin Amurka, Riley Moore, ya gana da tawagar Najeriya. Ya bayyana tattaunawar su kan yaki da ta’addanci da kare al’ummomin da ke cikin haɗari a matsayin “gaskiya, bayyananna, kuma mai amfani.”

Mambobin tawagar Najeriya sun haɗa da:
– Bianca Ojukwu, Karamin Ministan Harkokin Waje
– Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Kayode Egbetokun
– Babban Lauyan Tarayya, Lateef Fagbemi (SAN)
– Shugaban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Olatunbosun Oluyede
– Daraktan Leken Asiri na Tsaro, Laftanar Janar Emmanuel Undiendeye

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    Davido Meets IGP Disu, Seeks Enhanced Security Ahead of Osun Elections

    TheNy Tunji Braimoh,Abuja The Chairman of the Imole Youth Campaign Mobilisation Committee, David Adeleke, popularly known as Davido, has paid a courtesy visit to the Inspector-General of Police, Kayode Egbetokun…

    Delta NSCDC Launches Surveillance Task Force to Protect Critical National Infrastructure

    By Samson Emeka, Abuja TheNigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC), Delta State Command, has inaugurated a dedicated Critical National Assets and Infrastructure (CNAI) Monitoring and Surveillance Team as part…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Davido Meets IGP Disu, Seeks Enhanced Security Ahead of Osun Elections

    Davido Meets IGP Disu, Seeks Enhanced Security Ahead of Osun Elections

    Delta NSCDC Launches Surveillance Task Force to Protect Critical National Infrastructure

    Delta NSCDC Launches Surveillance Task Force to Protect Critical National Infrastructure

    Police Dismiss Reports of ‘Shoot-on-Sight’ Order, Clarify IGP’s Remarks on Illegal Firearms

    Police Dismiss Reports of ‘Shoot-on-Sight’ Order, Clarify IGP’s Remarks on Illegal Firearms

    PSM Editorial: The Politics of the N2 Billion Smear Campaign Against Mining Marshals

    PSM Editorial: The Politics of the N2 Billion Smear Campaign Against Mining Marshals

    Mining Marshals Petition Reps Speaker, Dismiss Corruption Allegations as Politically Motivated Smear CampaignWriting

    Mining Marshals Petition Reps Speaker, Dismiss Corruption Allegations as Politically Motivated Smear CampaignWriting

    Blood, Power and Billions: Why Violence Continues to Haunt Nigeria’s Transport Union System

    Blood, Power and Billions: Why Violence Continues to Haunt Nigeria’s Transport Union System