BABBAN KAMANDAN RUNDUNAR WUTA TA NIGERIA, SAMUEL OLUMODE, YA KADDAMAR DA KWAMITI DON KARFASA HADIN GWIWA TSAKANIN HUKUMA DA MASANA’ANTU

Babban Kwamandan Rundunar Wuta ta Tarayya, Olumode Adeyemi Samuel, ya kaddamar da Kwamitin Bita kan Hada-hadar Jama’a da Masana’antu (PPP) a Hedikwatar Rundunar da ke Abuja a yau.

Wannan mataki ya biyo bayan umarni daga Ministan Cikin Gida mai daraja, Dr. Olubunmi Tunji-Ojo, da aka bayar a taron Ministoci da aka gudanar a Suleja a watan Satumba, 2025, inda ya bukaci dukkan hukumomi karkashin Ma’aikatar su zurfafa hadin gwiwa da bangaren masu zaman kansu don inganta aiki da fadada tasirin ayyuka.

A cewar CGF, aikin kwamitin shi ne nazarin dukkan yarjejeniyoyin hadin gwiwa da ake da su, gano gibin aiwatarwa, kirkirar tsarin daidaito na hadin gwiwa a nan gaba, da kuma karfafa kula da dukkan ayyukan hadin gwiwa na Rundunar.

“Hadin gwiwa tsakanin Jama’a da Masana’antu shi ne ginshikin ci gaba da nasarar Rundunar Wuta ta Tarayya,” in ji CGF yayin kaddamarwar. “Yana ba mu damar amfani da kirkire-kirkire, kudade, da kwarewa don cika aikimmu yadda ya kamata.”

Haka kuma, ya jaddada cewa Rundunar na bude kofa ga sahihan hadin gwiwa a gida da kasashen waje, muddin sun yi daidai da manufa ta kare rayuka da dukiyoyi.

CGF Olumode ya yi kira ga mutane, kungiyoyi, da abokan ci gaba da su yi aiki tare da Rundunar Wuta ta Tarayya wajen inganta rigakafin gobara, ilimin tsaro, da karfafa ikon amsa gaggawa a al’ummomi. Ya bayyana cewa irin wannan hadin gwiwa zai rage asarar da gobara ke haifarwa, tallafawa ci gaban ingantattun ababen more rayuwa, da karfafa lafiyar kasa gaba daya.

An sa ran kwamitin zai gabatar da cikakken rahoto mai dauke da shawarwari masu aiki wanda zai sake fasalin dabarun hadin gwiwar Rundunar don amfanin kasa baki daya.

Wannan mataki na nuna ci gaba da jajircewar Rundunar wajen gaskiya, kirkire-kirkire, da manufofin zamani na Ma’aikatar Cikin Gida ta Tarayya.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    ENECHE OPPOSES CALLS FOR REMOVAL OF STATE SECURITY COMMANDANTS OVER INEFFICIENCY

    Share on Facebook Post on X Follow us

    BANDITS KILL NSCDC OFFICER, ABDUCT DAUGHTER

    Suspected bandits have killed an officer of the Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC), Mr. Ayo Olukotun, and abducted his daughter alongside several other residents during a violent attack…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    ENECHE OPPOSES CALLS FOR REMOVAL OF STATE SECURITY COMMANDANTS OVER INEFFICIENCY

    ENECHE OPPOSES CALLS FOR REMOVAL OF STATE SECURITY COMMANDANTS OVER INEFFICIENCY

    BANDITS KILL NSCDC OFFICER, ABDUCT DAUGHTER

    BANDITS KILL NSCDC OFFICER, ABDUCT DAUGHTER

    NSCDC Nasarawa Command Strengthens Security Partnership

    NSCDC Nasarawa Command Strengthens Security Partnership

    Did Handala Disrupt Israeli Radar Systems?

    Did Handala Disrupt Israeli Radar Systems?

    Whistleblower Accuses IBM, AT&T of Covering Up Breaches

    Whistleblower Accuses IBM, AT&T of Covering Up Breaches

    psm