Janar Komandan Hukumar Tsaron Jama’a ta Najeriya (NSCDC), Farfesa Ahmed Abubakar Audi, mni, OFR, ya jaddada kudirin hukumar na karfafa haɗin kai da gwamnati da kuma masu sarauta wajen inganta zaman lafiya, tsaron jama’a, da gina amana tsakanin jami’an tsaro da al’umma yayin ziyarar aikinsa zuwa Jihar Ekiti.
Da zarar ya isa Ado-Ekiti, Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG) ya tarbe shi a madadin Gwamnan Jihar, Mai Girma Mista Biodun Abayomi Oyebanji. Tattaunawar ta mayar da hankali kan yadda za a ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro, kare muhimman kadarorin kasa, da kuma karfafa rawar da al’umma ke takawa wajen tattara bayanan leƙen asiri.
Farfesa Audi ya bayyana godiya ga Gwamnatin Jihar Ekiti bisa goyon bayan da take bai wa hukumar, inda ya jaddada cewa ingantaccen tsaro yana ginuwa ne bisa amincewa da juna tsakanin jama’a da masu tsaron su.
“Tsaro aiki ne na kowa da kowa. Hukumar za ta ci gaba da ƙarfafa haɗin kai da hukumomin jihohi da masu sarauta domin tabbatar da cewa kowane ɗan Najeriya yana jin tsaro, ana ganin sa, kuma ana tallafa masa,” in ji Janar Komanda.
A ci gaba da ziyararsa, Farfesa Audi ya kai gaisuwa ta musamman ga Mai Martaba Oba (Dr.) Rufus Adeyemo Adejugbe Aladesanmi III, Ewi na Ado-Ekiti. Taron ya tattauna muhimmancin sarakuna wajen karfafa tsaro a matakin al’umma da tabbatar da zaman lafiya a ƙasa.
Ewi na Ado-Ekiti ya yaba da irin jagorancin da Janar Komanda Audi ke nunawa, inda ya bayyana NSCDC a matsayin hukumar tsaro mai kusanci da jama’a, wacce ke gina haɗin kai tsakanin ‘yan kasa da jami’an tsaro.
Ziyarar ta nuna imanin Farfesa Audi cewa ainihin tsaron kasa yana fitowa ne daga jama’a, yana ginuwa bisa haɗin kai, amincewa, da lura tare.




