Sojojin Najeriya Sun Ceto Mutane 21 da Aka Sace Yayin da Aikin FANSAN YAMA Ke Cigaba da Fatattakar ’Yan Bindiga a Jihohin Kwara da Kogi

Sojojin Rundunar 2 Division/Sector 3 na rundunar sojin Najeriya, karkashin Operation FANSAN YAMA, sun samu nasarar kubutar da mutane 21 da aka yi garkuwa da su a wani samame da aka gudanar a jihohin Kwara da Kogi, ranar 17 ga Oktoba, 2025.

Ayyukan hadin gwiwa da sojojin 12 Brigade Lokoja da 22 Armoured Brigade Ilorin suka gudanar, ya haifar da ceto mutane 14 maza, mata 5, jariri daya, da kuma ’yan kasar China 4. Rahotanni sun bayyana cewa wadanda aka ceto sun fito ne daga wurare daban-daban a cikin jihohin biyu. Sakamakon matsin lamba da sojoji suka kara kan ’yan bindigar, sai suka tilasta musu sakin wadanda suke tsare da su, wasu daga cikinsu sun shafe fiye da watanni hudu a hannunsu.

Babban Kwamandan Runduna ta 2 (GOC) kuma kwamandan Sector 3 Operation FANSAN YAMA, Manjo Janar C.R. Nnebeife, wanda ke jagorantar ayyukan, ya tabbatar da cewa an bai wa wadanda aka ceto kulawar gaggawa da kayan tallafi domin su murmure daga wahalhalun da suka sha a hannun ’yan bindigar. Ya jajanta musu tare da tabbatar da cewa rundunarsa za ta ci gaba da kai farmaki kan dukkanin ’yan ta’adda da masu aikata laifuka a yankin.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    Gombe Emerges Nigeria’s Most Secure State as Governor Inuwa Yahaya Receives National Security Leadership Award

    Pix: Gov. Yahaya Governor Muhammadu Inuwa Yahaya of Gombe State has been honoured with the prestigious 2026 Nigeria’s Most Secure State Excellence Award in recognition of his administration’s remarkable achievements…

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    The Management and Editorial Board of the People’s Security Monitor wishes to extend its profound and heartfelt appreciation to all distinguished guests, stakeholders, security leaders, partners, and participants who honoured…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Gombe Emerges Nigeria’s Most Secure State as Governor Inuwa Yahaya Receives National Security Leadership Award

    Gombe Emerges Nigeria’s Most Secure State as Governor Inuwa Yahaya Receives National Security Leadership Award

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Our Appreciation

    2026 PSM SECURITY SUMMIT: OUR APPRECIATION

    2026 PSM SECURITY SUMMIT: OUR APPRECIATION

    People’s Security Monitor Confers 2026 Exceptional Leadership Award on Ondo NSCDC Commandant Ibiloye…Dedicates Award to Ondo NSCDC Personnel

    People’s Security Monitor Confers 2026 Exceptional Leadership Award on Ondo NSCDC Commandant Ibiloye…Dedicates Award to Ondo NSCDC Personnel

    BREAKING: EMIR OF ARGUNGU CALLS FOR LEGAL COMMUNITY SELF-PROTECTION MEASURES AGAINST BANDITRY

    BREAKING: EMIR OF ARGUNGU CALLS FOR LEGAL COMMUNITY SELF-PROTECTION MEASURES AGAINST BANDITRY

    ONDO NSCDC Commandant Earns National Recognition for Exceptional Leadership in Civil Defence Operations

    ONDO NSCDC Commandant Earns National Recognition for Exceptional Leadership in Civil Defence Operations