Sojojin ruwa na Najeriya sun kara kaimi wajen yaki da satar danyen mai a yankin Neja Delta, inda suka lalata gidajen tace mai na fasa kaura guda shida tare da kwato kusan lita 11,200 na danyen mai da aka sace a wani jerin ayyuka da aka gudanar karkashin Operation Delta Sanity II.
Ayyukan wanda jami’an Forward Operating Base Escravos suka aiwatar na daga cikin kokarin rundunar ruwa na kare muhimman hanyoyin mai na kasa da hana barna ta tattalin arziki a yankin.
Da yake magana da manema labarai a birnin Warri ranar Juma’a, kwamandan Forward Operating Base Escravos, Kyaftin Ikenna Okoloagu, ya bayyana cewa nasarar da aka samu ta biyo bayan sahihan bayanan sirri da rundunar ta tattara ne.
Ya ce matsin lamba da rundunar ruwa ke ci gaba da yi wa masu fasa kauri na mai yana da nasaba da umarnin dabarun Shugaban Rundunar Ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ikechukwu Ogalla, wanda ya mayar da hankali wajen yaki da satar danyen mai, lalata bututun mai, da sauran ayyukan haramtattu a teku.
Okoloagu ya bayyana cewa a yayin aikin an rushe gidajen tace mai na fasa kaura guda shida inda aka gano lita 11,200 na danyen mai da aka sace a cikin rami 28 da kuma buhunan roba guda shida. Haka kuma an kwato injin famfo da masu fasa kauri ke amfani da shi.
A cikin bayanin cikakken aikin kwamandan ya ce an lalata gidajen tace mai na farko uku a ranar 2 ga Oktoba a kauyen Obodo Omadino da ke karamar hukumar Warri South-West inda aka kwato lita 3,750 na danyen mai daga ramuka goma da buhuna shida. A ranar 4 ga Oktoba an lalata wasu wurare biyu inda aka gano lita 1,450 na danyen mai daga ramuka biyar. A karshe a ranar 6 ga Oktoba an lalata wasu wurare biyu kuma aka gano lita 6,000 daga ramuka 13.
Kyaftin Okoloagu ya jaddada cewa wannan aiki yana goyon bayan kokarin Gwamnatin Tarayya na kara yawan fitar danyen mai a kullum da kuma rage barnar tattalin arziki da masu laifi ke yi. Ya tabbatar da cewa Forward Operating Base Escravos za ta ci gaba da lalata duk wani ginin tace mai na fasa kaura tare da kare kadarorin mai na kasar.
Ya kuma tunatar da cewa a watan Agusta rundunar ruwa ta lalata gidajen tace mai na fasa kaura guda goma a irin wadannan ayyuka a wani bangare na kokarinta na tabbatar da tsaro da tsaftar harkar man fetur a Najeriya.




