NSCDC Ta Kama Mai Safarar Wiwi a Kano, Ta Mika Wa Hukumar NDLEA Don Bincike

Hedikwatar Jihar Kano ta Hukumar Tsaro da Kare Muhimman Ababen Gwamnati (NSCDC) ta kama wani mutum da ake zargin mai safarar tabar wiwi ne, sannan ta mika shi ga Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) domin ci gaba da bincike da kuma daukar matakin doka.

Kwamandan Jihar Kano na NSCDC, Kwamanda Bala Bawa Bodinga, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar hukumar da ke Kano. Ya ce wannan kama na daga cikin kokarin hukumar wajen kawar da miyagu da masu safarar miyagun kwayoyi daga cikin al’umma.

A cewarsa, an kama wanda ake zargin ne a ranar Talata, 7 ga Oktoba, 2025, da misalin karfe 2:30 na safe, lokacin da jami’an NSCDC na sashen Doguwa suka samu sahihin bayanan sirri, suka tare babur da yake dauke da mutane uku da ake zargin suna safarar miyagun kwayoyi.

An gano wadanda ake zargin da sunaye Yusuf Alasan, mai shekaru 25, mazaunin garin Doguwa, tare da wasu mutum biyu, Muktar Musa da Musa Sani. Rahotanni sun nuna suna dauke da jakunkuna uku masu girman buhun sukari, cike da tabar wiwi, da ake kira Indian hemp ko Wiwi, suna jigilar ta daga Doguwa zuwa Kafau a karamar hukumar Doguwa ta Jihar Kano. An cafke su ne a kofar Riruwai cikin wannan karamar hukuma.

Kwamanda Bodinga ya ce an kammala binciken farko da hukumar ta gudanar, kuma bisa tsarin hadin kai tsakanin hukumomin tsaro, an mika wadanda ake zargin tare da kayan da aka kama ga Hukumar NDLEA ta Jihar Kano domin ci gaba da bincike da kuma aiwatar da matakan doka da suka dace.

Ya kuma jaddada cewa NSCDC a karkashin jagorancinsa za ta ci gaba da kare dukkan muhimman kadarorin kasa da kuma karfafa hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro wajen yakar miyagun ayyuka da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a Jihar Kano.

Kwamanda Bodinga ya gode wa kafafen yada labarai bisa goyon bayan da suke bayarwa a kai a kai, tare da kiran su da su ci gaba da hadin kai domin wayar da kan jama’a da kuma tabbatar da zaman lafiya a jihar.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    VGN Commander-General Endorses Federal Directive on Name Tags for Security Organisations

    The Commander-General of the Vigilante Group of Nigeria (VGN), Navy Captain A. B. Umar Bakori (retd), has expressed support for the Federal Government’s directive mandating private and voluntary security organisations…

    Nigerian Navy dismantles 22 illegal refineries, recovers 457,000 litres of stolen oil in three months

    The Nigerian Navy says it deactivated 22 illegal refining sites and recovered more than 457,000 litres of stolen crude oil and refined petroleum products between January and March 2026.The disclosure…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    VGN Commander-General Endorses Federal Directive on Name Tags for Security Organisations

    VGN Commander-General Endorses Federal Directive on Name Tags for Security Organisations

    Nigerian Navy dismantles 22 illegal refineries, recovers 457,000 litres of stolen oil in three months

    Nigerian Navy dismantles 22 illegal refineries, recovers 457,000 litres of stolen oil in three months

    Top 3 Cyber Insurance Incident Claims

    Top 3 Cyber Insurance Incident Claims

    Kyaftin ɗin Sojojin Ruwa Umar Bakori (mai ritaya), Shugaban Ƙasa na Ƙungiya/Janar Kwamanda, zai yi bayani kan “Raguwar Daukar Ma’aikata a Soja na Barazana ga Dimokiraɗiyyar Cikin Gida ta Najeriya”

    Kyaftin ɗin Sojojin Ruwa Umar Bakori (mai ritaya), Shugaban Ƙasa na Ƙungiya/Janar Kwamanda, zai yi bayani kan “Raguwar Daukar Ma’aikata a Soja na Barazana ga Dimokiraɗiyyar Cikin Gida ta Najeriya”

    Navy Captain Umar Bakori (Rtd), National Chairman/Commander General, to Speak on “Falling Military Recruitment Threatens Nigeria’s Internal Democracy”

    Navy Captain Umar Bakori (Rtd), National Chairman/Commander General, to Speak on “Falling Military Recruitment Threatens Nigeria’s Internal Democracy”

    NIGERIAN AND SOUTH AFRICAN NAVIES CONCLUDE FIRST EVER STAFF TALKS TO DEEPEN MARITIME SECURITY COOPERATION

    NIGERIAN AND SOUTH AFRICAN NAVIES CONCLUDE FIRST EVER STAFF TALKS TO DEEPEN MARITIME SECURITY COOPERATION