Rundunar Sojojin Najeriya ta tura cikakken runduna tare da manyan kayan aikin yaki zuwa muhimman yankuna a mazabar Kwara ta Kudu domin kara karfafa yaki da matsalar rashin tsaro a jihar.
Sojoji sun fara gudanar da manyan ayyukan tsaro a kauyuka da ke kewaye da Oke Ode da Babanla, duka a karamar hukumar Ifelodun, tare da wasu yankuna na karamar hukumar Edu da Patigi. Sojojin na gudanar da bincike a cikin dazuzzuka masu kauri da ake zargin masu garkuwa da mutane ke boyewa, wadanda suka kai hare-hare da sace-sace a watannin baya-bayan nan.
Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, wanda ya gana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan batun tsaro a karshen mako a Jos, ya yaba wa Shugaban kasa, manyan hafsoshin soji da sauran hukumomin tsaro bisa saurin daukar mataki da kuma jajircewarsu wajen dawo da zaman lafiya a fadin jihar.
A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Rafiu Ajakaye, ya fitar a ranar Laraba, gwamnan ya tabbatar da kudirin gwamnati na ci gaba da bayar da goyon baya ga dukkan hukumomin tsaro da ke cikin aikin.
Ya ce gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tallafa wa sojoji, DSS, yan sanda da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma a Kwara.
Gwamnan ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa aikin tsaron da aka lakaba masa suna Operation Fasan Yanma zai iya kawar da dukkan barazanar tsaro a yankunan da abin ya shafa, musamman a Kwara ta Kudu da Kwara ta Arewa.
Ya kuma gode wa Shugaba Bola Tinubu da hukumomin tsaro bisa jajircewarsu da kokarinsu na kawo karshen matsalolin tsaro, tare da jaddada bukatar kara zage damtse wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Gwamnan ya nuna tabbaci cewa rundunar sojoji karkashin jagorancin Brigadier Janar A.A. Babatunde za ta samu nasara wajen cika wannan muhimmin aiki.
Haka kuma, Gwamna AbdulRazaq ya yaba wa Ofishin Mai Ba da Shawara kan Tsaron Kasa, Babban Hafsan Sojojin Kasa, Babban Jami’in da ke jagorantar Runduna ta 2, da sauran manyan hafsoshin soji bisa hadin kai da goyon bayansu wajen tabbatar da dorewar zaman lafiya da tsaro a Jihar Kwara.




