NSCDC Ta Ƙarfafa Haɗin Gwiwa da Sojojin Sama na Najeriya da Ma’aikatar Shari’a a Jihar Katsina

Kwamandan Jihar Katsina na Hukumar Tsaro ta Najeriya (NSCDC), Commandant of Corps A.D. Moriki Acti Anim, a ranar Laraba 8 ga Oktoba, 2025, ya kai ziyarar ban girma ga Kwamandan Rundunar 213 Forward Operating Base na Sojojin Sama dake Katsina, wanda kuma shi ne Shugaban Rundunar Hadin Gwiwar Iskar Sama ta Ayyukan Hadarin Daji, Sashen II, Air Commodore G.I. Jibia, da kuma Kwamishinar Shari’a wato Babbar Lauya ta Jihar Katsina, Hajiya Fadila Mohammed Dikko. Ziyarar ta gudana ne a sansanin Sojojin Sama dake kan hanyar Daura da kuma Ofishin Ma’aikatar Shari’a dake kan hanyar Kano, duka a cikin garin Katsina.

A yayin ziyarar, Commandant Moriki ya jaddada kudirin Babban Kwamandan NSCDC, Farfesa Ahmed Abubakar Audi, na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa tare da kare muhimman gine-gine da kadarorin gwamnati a fadin kasar. Ya bayyana cewa wannan ziyara tana cikin shirin sada zumunta domin ƙarfafa haɗin kai, fahimtar juna da haɗin gwiwa mai ɗorewa tsakanin NSCDC, Sojojin Sama da Ma’aikatar Shari’a. Haka kuma, ya nuna godiya ga shugabannin biyu bisa kyakkyawar tarbar da suka yi masa tare da tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da bada goyon baya wajen cimma burin tsaro na bai daya.

A nasa jawabin, Air Commodore G.I. Jibia da Hajiya Fadila Mohammed Dikko sun taya Commandant Moriki murna bisa sabon nadin sa a Jihar Katsina, tare da yabawa hukumar NSCDC bisa kwazon ta da jajircewar ta wajen kare lafiya da tsaron al’umma. Sun kuma tabbatar da shirin su na ƙara ƙarfafa dangantaka mai kyau da inganta haɗin kai tsakanin hukumomi domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin jihar.

Daga cikin abubuwan da suka wakana a ziyarar har da musayar kyaututtuka, tattaunawar aiki kan batun tsaro da kuma ɗaukar hotunan haɗin kai da suka nuna girmamawa da amincewar juna tsakanin hukumomin.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    MC Oluomo Challenges Adeleke’s Suspension of NURTW in Osun, Says Governor Lacks Legal Authority

    By Samson Chinedu, Abuja The National President of the National Union of Road Transport Workers (NURTW), Alhaji Musiliu Akinsanya, popularly known as MC Oluomo, has rejected the decision of Osun…

    NIS Comptroller-General Charges Public Relations Officers to Enhance Service Delivery Through Professional Training

    By Tunji Braimoh, Abuja The Comptroller-General of the Nigeria Immigration Service (NIS), Kemi Nanna Nandap, on Thursday encouraged public relations officers of the Service participating in the ongoing Special Executive…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    MC Oluomo Challenges Adeleke’s Suspension of NURTW in Osun, Says Governor Lacks Legal Authority

    MC Oluomo Challenges Adeleke’s Suspension of NURTW in Osun, Says Governor Lacks Legal Authority

    NIS Comptroller-General Charges Public Relations Officers to Enhance Service Delivery Through Professional Training

    NIS Comptroller-General Charges Public Relations Officers to Enhance Service Delivery Through Professional Training

    NSCDC Reaffirms Commitment to Maritime Security, Inter-Agency Cooperation at UNODC VBSS Training

    NSCDC Reaffirms Commitment to Maritime Security, Inter-Agency Cooperation at UNODC VBSS Training

    Benin Airport Incident: Fire Service Boss Praises Firefighters for Swift Rescue of Passengers

    Benin Airport Incident: Fire Service Boss Praises Firefighters for Swift Rescue of Passengers

    NSCDC Delta, ICPC Strengthen Partnership Against Corruption

    NSCDC Delta, ICPC Strengthen Partnership Against Corruption