Hukumar Nigeria Security and Civil Defence Corps reshen Jihar Sokoto ta yi kakkausar gargaɗi ga kamfanonin gine gine da masu haɓaka ayyuka kan haƙa ƙasa ba tare da tsari ba, lamarin da ya haddasa yawan lalacewar wayoyin fibre optic da sauran muhimman kayayyakin more rayuwa a faɗin jihar.
A cikin wata sanarwar manema labarai mai kwanan wata 21 ga Fabrairu, 2026, mai lamba AAS 15 NSCDC PRU SSC VOL.27.6, rundunar ta bayyana cewa yawaitar katsewar sadarwa a jihar na da alaƙa da lalata wayoyin fibre optic a wuraren aikin gina tituna.
Sanarwar ta ce matakin ya yi daidai da manufar kare Muhimman Kayayyakin Ƙasa ta shekarar 2024, ƙarƙashin jagorancin Office of the National Security Adviser, wadda ta bai wa hukumar NSCDC alhakin kare muhimman kayayyakin ƙasa ciki har da na sadarwa.
Da yake jawabi a wani taron haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki, Kwamandan Jiha, EA Ajayi, ya jaddada muhimmancin dakile haƙa ƙasa ba bisa ƙa’ida ba da kamfanonin gine gine ke yi a jihar.
Ya ce ci gaba da lalata wayoyin fibre optic na janyo katsewar intanet, ayyukan bankuna, harkokin kasuwanci da sauran muhimman ayyuka, wanda hakan ke kawo cikas ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewa a Jihar Sokoto.
Ajayi ya buƙaci dukkan kamfanonin gine gine da sauran masu ruwa da tsaki su guji haƙa ƙasa ba tare da yin binciken kayan more rayuwa da ke ƙarƙashin ƙasa da tabbatar da inda aka shimfiɗa su ba kafin fara aiki.
A yayin tattaunawar, ya bayyana cewa kare muhimman kayayyakin ƙasa ba ya taƙaita ga ɓangaren sadarwa kaɗai ba, har ma ya shafi wutar lantarki, man fetur da iskar gas, lafiya da makamashi. Ya yi gargaɗin cewa ba za a lamunci duk wani nau’in ɓarna ga wayoyin fibre optic, layukan dogo, wutar lantarki, hasumiyoyin sadarwa da rijiyoyin manhole ba.
Ya ƙara da cewa rundunar za ta ƙara wayar da kan jama’a ta rediyo da sauran kafafen yaɗa labarai domin tabbatar da fahimtar al’umma kan muhimmancin kare kayayyakin ƙasa.
Rundunar ta kuma tabbatar wa masu ruwa da tsaki da kudurinta na yin aiki tare da kamfanonin samar da sabis na sadarwa domin tantance sahihan taswirorin wuraren da aka shimfiɗa kayayyakin sadarwa a faɗin jihar. An bayyana cewa wannan haɗin gwiwa zai ƙarfafa tsarin tsaro gaba ɗaya da kare muhimman kayayyakin more rayuwa.
A ƙarshe, Ajayi ya jaddada cewa a wannan zamani na bunƙasar fasahar zamani da haɗin kan duniya, kayayyakin sadarwa na taka muhimmiyar rawa wajen tsaron ƙasa, daidaiton tattalin arziki da ci gaban ƙasa, yana mai kira ga kowa da kowa da ya ɗauki alhakin kare su domin su ne ginshiƙan ci gaban al’umma.



