NSCDC TA LA’ANTA ZANGA-ZANGAR ADAWA DA GWAMNATI, TA NEMI ƘARIN HADA KAI TSAKANIN MASU RUWA DA TSARO DOMIN KARE MUHIMMAN ABUBUWAN GININ ƘASA

Hukumar Tsaro ta Ƙasa da Kare Fararen Hula (NSCDC) ta bayyana la’antar ta kan matakin wasu masu zanga-zangar adawa da gwamnati da suka taru a gaban hedikwatar hukumar da ke Abuja da safiyar yau ƙarƙashin sunan neman adalci.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Ƙasa na hukumar, Babban Superintendent na Corps (CSC) Babawale Afolabi ya fitar, NSCDC ta bayyana cewa mamayar da sama da mutane 50 suka yi a kofar shiga hedikwatar ta Corps abin ƙyama ne kuma sabawa doka. Ya bayyana cewa masu zanga-zangar sun rika rera wakokin adawa da gwamnati tare da tayar da hayaniya a wajen aiki.

CSC Afolabi ya ce Kwamandan Janar na NSCDC, Farfesa Ahmed Abubakar Audi, ya riga ya aika da gargaɗin tsaro ga dukkan kwamandojin jihohi da sauran sassan hukumar, yana umartar jami’ai da su kasance cikin shiri da kuma ƙara ƙaimi wajen kare Muhimman Abubuwan Ginin Ƙasa. Wannan umarni ya biyo bayan rahotannin leƙen asiri da suka nuna cewa wasu kungiyoyi na shirin yin zanga-zanga domin nuna goyon baya ga shugaban IPOB da ake tsare da shi, Nnamdi Kanu.

Ya bayyana cewa an riga an tura jami’an leƙen asiri da na sanye da kayan aiki zuwa jihohi da Babban Birnin Tarayya (FCT) domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi. Ya jaddada cewa hukumar ba za ta lamunci duk wata barna, tashin hankali, ko yunkurin ɓata zaman lafiya ba, musamman ganin cewa kotu ta riga ta haramta wannan zanga-zangar.

Yayin da yake sake tabbatar da manufar hukumar, CSC Afolabi ya ce NSCDC tana nan daram wajen kare Muhimman Abubuwan Ginin Ƙasa, gudanar da aikin agajin gaggawa, sa ido kan kamfanonin tsaro masu zaman kansu, da kuma kare manoma da gonakinsu domin inganta tsaron abinci a fadin ƙasa.

Ya ƙara da cewa kodayake ‘yan ƙasa na da ‘yancin gudanar da taro cikin lumana bisa kundin tsarin mulki, wajibi ne a yi hakan cikin bin doka da oda. NSCDC, in ji shi, za ta ci gaba da yin aiki tare da sauran hukumomi masu ruwa da tsaki domin kare kadarorin ƙasa, tare da gargadin cewa duk wanda aka samu da laifin tayar da zaune tsaye ko lalata kadarori zai fuskanci cikakken hukunci bisa doka.

  • Keji Mustapha

    Related Posts

    psm

    Share on Facebook Post on X Follow us

    Fight Against Terror Is a Collective National Responsibility, Not Military Alone — Tinubu

    President Bola Tinubu has commended Nigeria’s security personnel for their bravery and sacrifices in confronting terrorism, banditry, kidnapping, and other security challenges across the country. In a statement shared on…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    psm

    Fight Against Terror Is a Collective National Responsibility, Not Military Alone — Tinubu

    Why I Was in a Hurry to Establish the NSCDC Mining Marshals — Dele Alake

    Why I Was in a Hurry to Establish the NSCDC Mining Marshals — Dele Alake

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Grassroots Intelligence Key to Protecting Citizens, Security Personnel — NOA DG

    2026 People’s Security Monitor Security Summit: Grassroots Intelligence Key to Protecting Citizens, Security Personnel — NOA DG

    NAF Deploys Surveillance Aircraft to Aid Rescue of Abducted Oyo Teachers, Pupils

    NAF Deploys Surveillance Aircraft to Aid Rescue of Abducted Oyo Teachers, Pupils

    Police Arrest Four Suspects, Kill Two in Rescue Operation for Adelabu’s Sister in Ibadan

    Police Arrest Four Suspects, Kill Two in Rescue Operation for Adelabu’s Sister in Ibadan