A cikin sabon yunƙuri na haɗin kai don dakile matsalar haƙar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a fadin ƙasa, kwamitin wucin gadi na Majalisar Wakilai kan Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba ya jaddada haɗin gwiwarsa da Hukumar Tsaro ta Jama’a da Kare Muhalli (NSCDC), yana bayyana dakarun “Mining Marshals” na hukumar a matsayin muhimmin ɓangare wajen tsaftace sashen ma’adanai na ƙasa.
Yayin ƙaddamar da kwamitin a harabar Majalisar Dokoki ta Ƙasa da ke Abuja, mambobin Majalisar sun jaddada buƙatar ƙara haɗin kai tsakanin aikin sa ido na majalisa da kuma matakan aiwatarwa na hukumomin tsaro domin rushe ƙungiyoyin da ke gudanar da haƙar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, waɗanda suka jawo wa ƙasar asarar makudan kudade da lalacewar muhalli.
Masu sharhi sun bayyana wannan mataki a matsayin babban ci gaba na manufofi — wanda zai haɗa wakilan majalisa, hukumomin tsaro da masu tsara dokoki domin dawo da tsari, gaskiya da inganci a harkar ma’adanai.
Dakarun “Mining Marshals” na NSCDC, waɗanda aka horar musamman domin sa ido da tabbatar da bin ƙa’ida a harkar haƙar ma’adanai, sun taka muhimmiyar rawa wajen fatattakar masu haƙar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a sassan ƙasar, suna taimakawa wajen kare dukiyar ma’adanan ƙasa daga ɓarayin da ke amfani da hanyoyin da ba su dace ba.
Bangarorin biyu sun yi alkawarin ƙarfafa haɗin gwiwa ta hanyar musayar bayanan leƙen asiri, gudanar da ayyuka tare a filin aiki, da kuma tallafawa gyaran dokoki domin tabbatar da cewa duk wanda aka kama da laifi zai fuskanci hukunci mai tsanani.
Masana sun bayyana wannan haɗin gwiwa a matsayin muhimmin mataki da zai taimaka wajen tabbatar da dorewar sarrafa albarkatun ƙasa da kuma ƙarfafa tsaron tattalin arzikin Najeriya.




