A wani muhimmin mataki bayan karbar ragamar aiki, Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, Tunji Disu, ya kaddamar da wani babban kwamiti da zai tsara tsarin aiki na rundunar ‘yan sanda da jihohi za su rika sarrafawa a fadin kasar.
Wannan mataki ya biyo bayan umarnin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, wanda kwanan nan ya bukaci Majalisar Dokokin Kasa ta gaggauta yin gyaran kundin tsarin mulki domin bai wa jihohi damar kafa nasu rundunar ‘yan sanda. Shugaban kasar ya sha nanata cewa raba ikon aikin ‘yan sanda zuwa matakin jihohi zai taimaka wajen saurin mayar da martani ga matsalolin tsaro tare da karfafa tsaro a matakin al’umma.
Da yake jawabi a lokacin kaddamar da kwamitin a Abuja, Disu ya bayyana cewa an dora wa kwamitin alhakin samar da ingantaccen tsari mai amfani ga ‘yan sandan jihohi. Ya ce kwamitin zai nazarci yadda ake gudanar da aikin ‘yan sanda a wasu kasashe masu nasara, ya tsara ka’idoji bayyanannu na daukar ma’aikata da horaswa, sannan ya bayar da shawarwari kan hanyoyin sa ido da za su kara tabbatar da gaskiya da amincewar jama’a. Haka kuma zai gabatar da shawarwari kan hanyoyin samun kudaden da za su dore tare da tsara dabarun hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaron tarayya da na jihohi.
Sufeto Janar din ya jaddada cewa kafa ‘yan sandan jihohi bai kamata a dauke shi a matsayin barazana ga rundunar tarayya ba, sai dai a gan shi a matsayin hadin gwiwa da zai kara karfafa tsaron kasa. Ya ce sabon tsarin zai kara karfafa aikin ‘yan sanda na kusanci da al’umma, ya inganta gano barazanar tsaro tun da wuri, sannan ya fadada karfin hukumomin tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Farfesa Olu Ogunsakin, Darakta Janar na Cibiyar Nazarin ‘Yan Sanda ta Kasa, shi ne shugaban kwamitin, yayin da Kwamishinan ‘Yan Sanda Bode Ojajuni ke matsayin sakatare. Mambobin kwamitin sun hada da manyan jami’an ‘yan sanda masu aiki da kuma wadanda suka yi ritaya, domin a hada ilimin bincike na jami’a da kuma kwarewar aiki a fili.
Daya daga cikin wadanda suka yi maraba da wannan mataki shi ne tsohon Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda Ali Amodu mai ritaya, wanda ya ce tun a shekarar 1981 yake goyon bayan ra’ayin raba ikon aikin ‘yan sanda zuwa matakin jihohi. Ya bayyana cewa ingantaccen aikin ‘yan sanda dole ne ya dace da yanayin rayuwar al’umma, yana mai cewa jami’an da suka fahimci al’adu da tsarin zamantakewar yankunansu sun fi iya hana aikata laifuka.
Shi ma tsohon Kwamishinan ‘Yan Sanda Lawrence Alobi ya jaddada muhimmancin fayyace dangantaka tsakanin ‘yan sandan jihohi da na tarayya. Ya ce wajibi ne kwamitin ya tsara ka’idoji da za su jagoranci hadin gwiwa a lokutan da binciken laifuka ya wuce iyakokin jiha zuwa wata jiha.
Har ila yau Disu ya bayyana cewa rundunar ‘yan sanda na sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa a Gabas ta Tsakiya, musamman rikice rikicen da suka shafi Amurka, Isra’ila da Iran. Ya ce rundunar ta kara kaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma sintiri a sassa daban daban na kasar domin hana rikice rikicen kasashen waje haddasa tashin hankali ko ramuwar gayya a cikin Najeriya.



